ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiyoyin Ma’aikatan Jami’o’i SSANU Da NASU Sun Janye Yajin Aikin Gargadi Da Suka Shiga

by Muhammad
2 years ago
SSANU

Kungiyar manyan ma’aikatan jami’o’in Nijeriya (SSANU) ta sanar da kawo karshen yajin aikin gargadi na kwanaki bakwai, domin bai wa gwamnati damar yin abin da ya kamata.

Shugaban kungiyar, Mohammed Ibrahim, ne ya bayyana hakan a wani taron masu ruwa da tsaki, wanda kungiyar marubutan ilimi ta Nijeriya (EWAN) ta shirya ranar Lahadi a Legas.

  • Yadda Kungiyar SSANU Da NASU Suka Gudanar Da Zanga-zangar Lumana A Zariya
  • Yajin Aikin ASUU: Malamin Jami’a Ya Yi Barazanar Ajiye Aiki Kan Rashin Albashi

Taron wanda ya samu halartar shugaban kungiyar ma’aikatan da ba masu koyarwa ba (NASU), Mista Ibeji Nwokoma, yajin aikin wanda aka yi kan rashin bashin albashi da ma’aikatan ke bi.

ADVERTISEMENT

Idan za a iya tunawa, kwamitin hadin guiwa na kungiyoyin kwadago na jami’o’in da abin ya shafa, a ranar 18 ga watan Maris, ya umarci mambobin kungiyar da su tsunduma yajin aikin gargadi kan hana su albashi na watanni hudu da kuma rashin aiwatar da yarjejeniyar da suka kulla da gwamnatin tarayya a shekarar 2009.

“Mun yi taro da wakilan gwamnatin tarayya a Abuja a ranar Laraba kuma babu wani abu da a zahiri da ya fito dangane da batun.

LABARAI MASU NASABA

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

“Eh, sun yarda da cewa muna yajin aikin ne kuma matakin ya gurgunta ayyukan da ake yi a harabar jami’o’in tarayya.

“Don haka taron ba komai ba ne illa neman a dakatar da yajin aikin, yayin da suka gaza yin wani abu cikin gaggawa.

“Za a kawo karshen yajin aikin da karfe 12 na dare. Za mu koma rassanmu daban-daban domin duba sakamakon yajin aikin gargadin, da kuma taron da aka yi da gwamnatin tarayya a baya-bayan nan, daga nan kuma za mu yi duba kan mataki na gaba.” Cewar Ibrahim

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani
Manyan Labarai

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
HOTUNA: Yadda Tinubu Ya Kai Ziyara Don Ta’aziyyar Sheikh Dahiru Bauchi
Hotuna

HOTUNA: Yadda Tinubu Ya Kai Ziyara Don Ta’aziyyar Sheikh Dahiru Bauchi

December 20, 2025
Next Post
Malaman Musulunci Suna Taro A Makkah Kan Ƙarfafa Samar Da Haɗin Kai A Tsakanin Musulmi

Malaman Musulunci Suna Taro A Makkah Kan Ƙarfafa Samar Da Haɗin Kai A Tsakanin Musulmi

LABARAI MASU NASABA

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025
Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

December 20, 2025
An Nuna Jigo Da Tambarin Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Shekarar 2026 A Moscow

An Nuna Jigo Da Tambarin Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Shekarar 2026 A Moscow

December 20, 2025
Auren Da Ya Fi Auren Gidan Daula Dadi Ga Mace

Auren Da Ya Fi Auren Gidan Daula Dadi Ga Mace

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.