• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Dukufa Magance Matsalolin Bangaren Lantarki, In Ji Minista

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
Tashar Lantarki Da Kamfanin Kasar Sin Ta Gina A Botswana Ta Baiwa Kasar Damar Fitar Da Lantarki Zuwa Makwafta
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin tarayya ta ce ta dukufa wajen ganin ta shawo kan asalin matsalolin da suke addabar bangaren wutar lantarki tare da nemo mafita a kansu.

Ministan wutan lantarki, Adebayo Adelabu shi ne ya shaida hakan a lokacin da ke ganawa da ‘yan jarida jim kadan bayan ganawa da ya yi da wasu masu ruwa da tsakani na jam’iyyar APC a sakateriyar jam’iyyar na Jihar Oyo da ke Oke-Ado a Ibadan.

  • Abubuwa 10 Da Ya Kamata A Sani Game Da Sabon Tsarin Biyan Kudin Wutar Lantarki
  • Matsanancin Rashin Lantarki Ya Addabi ‘Yan Nijeriya

Ministan ya ce Shugaban kasa, Bola Tinubu ya himmatu wajen kawo gagarumin sauyi a bangaren wutar lantarki.

Ya ce, “Bari na yi amfani da wannan damar na tabbatar wa al’ummar Nijeriya cewa gwamnatin Bola Tinubu a shirye take wajen ganin ta sauya abubuwan da suke faruwa a harkar wutar lantarki, ta canja takun da ke bangaren. Wannan dalilin ne ya sa yanzu muka dukufa wajen shawo kan asalin matsalolin wutar lantarki.

“Muna yin wannan aikin shawo kan dukkanin matsalolin ne tare da yin aikin hadin guiwa da dukkanin masu ruwa da tsaki a bangaren domin nemo mafita, kama daga bangaren samar da gas zuwa tarawa, watsawa da kuma rarraba wutar lantarki hadi da su kansu kwastomomi masu amfani da lantarkin. Akwai abubuwa da dama da muke yi kuma abubuwa za su fara canzawa.”

Labarai Masu Nasaba

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

Ya ce a yanzu ma akwai ci gaba da ake samu a wasu wuraren, amma yanzu ma aka fara samun shawo kan lamura ta yadda ‘yan Nijeriya za su mori lantarki fiye da yadda suke tunani cikin rahusa da kuma inganci a wadace.

Adebayo ya roki ‘yan Nijeriya da su kara hakuri da gwamnatin Tinubu, yana mai cewa halin da ake ciki na wucin gadi ne lamura za su sauya nan ba da jimawa ba.

“Ni kaina na himmatu wajen ganin na shawo kan matsalolin da suke bangaren wutar lantarki, kuma tabbas a kwanan nan ‘yan Nijeriya za su fara rausayawa suna murna da ci gaba da za mu kawo a bangaren,” ya shaida.

Da yake magana kan kokarin gwamnati na shawo kan matsalar karancin mita a Nijeriya, ministan ya ce shugaban kasa ya kafa kwamitin kula da lamuran mita, kuma sun himmatu wajen samar da sama da biliyan 75 domin tabbatar da akalla mita guda miliyan 2 an sanyasu nan da shekaru biyar masu zuwa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Raba Tallafi Ba Zai Fitar Da ‘Yan Nijeriya Daga Kangin Rayuwa Ba – Gwamna Diri

Next Post

Kamfanonin Sin Sun Kara Kirkiro Sabbin Kayayyaki Masu Lambar Kira

Related

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

6 minutes ago
Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

10 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

12 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

13 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

13 hours ago
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu
Labarai

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

15 hours ago
Next Post
Kamfanonin Sin Sun Kara Kirkiro Sabbin Kayayyaki Masu Lambar Kira

Kamfanonin Sin Sun Kara Kirkiro Sabbin Kayayyaki Masu Lambar Kira

LABARAI MASU NASABA

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.