ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwa 10 Da Ya Kamata A Sani Game Da Sabon Tsarin Biyan Kudin Wutar Lantarki

by Sadiq
2 years ago
Wutar Lantarki

Gwamnatin Tarayya ta sanar da karin kudin wutar lantarki da ‘yan Nijeriya ke biya, wanda hakan ya haifar da cece-kuce a tsakanin mutane.

Hukumar kula da wutar lantarki ta Nijeriya (NERC), ta yi karin kashi 240 cikin 100 na kudin wutar lantarki da ‘yan Nijeriya ke biya, inda ta ce hakan zai ba ta damar biyan kudin gas da kuma sauran gyare-gyaren injina da suka shafi rarraba wutar lantarki.

  • Hukumar Kashe Gobara Ta Ceto Mutane 12 Da Dukiyar Miliyan 130 A Kano
  • Za Mu Sa Kafar Wando Daya Da Masu Digirin Bogi A Nijeriya – Minista

LEADERSHIP ta yi duba kan yadda sabon tsarin biyan kudin wutar lantarki zai kasance da kuma mutanen da ya shafa.

ADVERTISEMENT

NERC ta kara farashin kudin wutar lantarkin kan Naira 225 kan kowane kilowat a awa daya, amma wannan kari zai shafi iya wadanda suke kan rukunin samun wuta na ‘A’ ne kadai.

Hukuncin dai na zuwa ne, daidai lokacin da ake fama da matsalar rashin wutar lantarki a fadin kasar nan.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

Ga yadda tsarin biyan kudin wutar lantarkin zai kasance:

1.NERC ta amince da karin farashin wutar lantarki da kashi 240 ga kwastomomin da ke rukunin ‘A’, wanda kudin ya tashi daga Naira 66 zuwa Naira 225 a kowace awa daya.

2. Wannan karin ya shafi kwastomomin da ke samun wutar lantarki na awa 20 ko sama da haka, wadanda ke kan hanyoyin samar da wuta 481 daga 3,000, wanda ke wakiltar kashi 15 na mutanen da ke amfani da wutar lantarki a Nijeriya.

3. Masu amfani da wutar lantarkin da ba sa samun wutar awa 20 a rana, dole NERC za ta rage yawan abin da za su ke biya tare da sauya musu rukuni.

4. Wadanda suke kan rukunin ‘A’ za su fuskanci gagarumin karin farashin kudin wutar lantarki wanda zai iya tashi daga N50,000 zuwa N170,000 duk wata, amma ya danganta da yadda suka yi amfani da lantarkin.

5. Kwastomomin da ke kan rukunin ‘A’ ne kadai ke da tabbacin samun wutar lantarkin akalla awa 20 daga kamfanonin rarraba wutar lantarki guda 11, kamar yadda NERC ta bayyana.

6. Kwastomomin da ke kan rukunin ‘B’, ‘C’, ‘D’, da ‘E’, wadanda ke samun wutar lantarkin kasa da awa 20, karin kudin ba zai shafe su ba.

7. Karin kashi 240 na nufin gwamnati ta cire tallafin wutar lantarki gaba daya a kan kwastomomin da ke rukunin ‘A’, wadanda ke wakiltar kashi 15 na masu amfani da wutar lantarki, sannan kashi 40 na wutar lantarkin da ake rarrabawa a fadin kasar nan.

8. An kaddamar da karin ne a ranar Laraba, 3 ga watan Afrilu, 2024, wanda ke nufin kwastomomin rukunin ‘A’ ne kadai karin kashin 240 na wutar lantarki zai shafa.

9. Duk da karin kudin wutar lantarkin da aka yi, amma kwastomomi na fuskantar koma baya na samun wuta tun daga watan Janairu 2024, wanda ministan wutar lantarki, Adebayo Adelabu ya danganta lamarin da karancin gas da ake fama da shi a kasar nan.

Sai dai wannan kari na kudin wutar lantarki da gwamnati ta yi, zai ta’allaka ne gaba daya da wutar da kwastomomi ke samu a rana, wanda da shi ne kadai za a yi alkalacin abin da za su biya duk wata.

10. Wadanda suke kan rukunin ‘A’ za a iya dawo da su wani rukunin matukar ba sa samun wutar lantarkin awa 20 a kowace rana.

MASU ALAKA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Next Post
Bloomberg: Damuwa Game Da Karfin Sin Wajen Samar Da Hajoji Ba Ta Da Tushe

Bloomberg: Damuwa Game Da Karfin Sin Wajen Samar Da Hajoji Ba Ta Da Tushe

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.