ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwa 10 Da Ya Kamata A Sani Game Da Sabon Tsarin Biyan Kudin Wutar Lantarki

by Sadiq
2 years ago
Wutar Lantarki

Gwamnatin Tarayya ta sanar da karin kudin wutar lantarki da ‘yan Nijeriya ke biya, wanda hakan ya haifar da cece-kuce a tsakanin mutane.

Hukumar kula da wutar lantarki ta Nijeriya (NERC), ta yi karin kashi 240 cikin 100 na kudin wutar lantarki da ‘yan Nijeriya ke biya, inda ta ce hakan zai ba ta damar biyan kudin gas da kuma sauran gyare-gyaren injina da suka shafi rarraba wutar lantarki.

  • Hukumar Kashe Gobara Ta Ceto Mutane 12 Da Dukiyar Miliyan 130 A Kano
  • Za Mu Sa Kafar Wando Daya Da Masu Digirin Bogi A Nijeriya – Minista

LEADERSHIP ta yi duba kan yadda sabon tsarin biyan kudin wutar lantarki zai kasance da kuma mutanen da ya shafa.

ADVERTISEMENT

NERC ta kara farashin kudin wutar lantarkin kan Naira 225 kan kowane kilowat a awa daya, amma wannan kari zai shafi iya wadanda suke kan rukunin samun wuta na ‘A’ ne kadai.

Hukuncin dai na zuwa ne, daidai lokacin da ake fama da matsalar rashin wutar lantarki a fadin kasar nan.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Ga yadda tsarin biyan kudin wutar lantarkin zai kasance:

1.NERC ta amince da karin farashin wutar lantarki da kashi 240 ga kwastomomin da ke rukunin ‘A’, wanda kudin ya tashi daga Naira 66 zuwa Naira 225 a kowace awa daya.

2. Wannan karin ya shafi kwastomomin da ke samun wutar lantarki na awa 20 ko sama da haka, wadanda ke kan hanyoyin samar da wuta 481 daga 3,000, wanda ke wakiltar kashi 15 na mutanen da ke amfani da wutar lantarki a Nijeriya.

3. Masu amfani da wutar lantarkin da ba sa samun wutar awa 20 a rana, dole NERC za ta rage yawan abin da za su ke biya tare da sauya musu rukuni.

4. Wadanda suke kan rukunin ‘A’ za su fuskanci gagarumin karin farashin kudin wutar lantarki wanda zai iya tashi daga N50,000 zuwa N170,000 duk wata, amma ya danganta da yadda suka yi amfani da lantarkin.

5. Kwastomomin da ke kan rukunin ‘A’ ne kadai ke da tabbacin samun wutar lantarkin akalla awa 20 daga kamfanonin rarraba wutar lantarki guda 11, kamar yadda NERC ta bayyana.

6. Kwastomomin da ke kan rukunin ‘B’, ‘C’, ‘D’, da ‘E’, wadanda ke samun wutar lantarkin kasa da awa 20, karin kudin ba zai shafe su ba.

7. Karin kashi 240 na nufin gwamnati ta cire tallafin wutar lantarki gaba daya a kan kwastomomin da ke rukunin ‘A’, wadanda ke wakiltar kashi 15 na masu amfani da wutar lantarki, sannan kashi 40 na wutar lantarkin da ake rarrabawa a fadin kasar nan.

8. An kaddamar da karin ne a ranar Laraba, 3 ga watan Afrilu, 2024, wanda ke nufin kwastomomin rukunin ‘A’ ne kadai karin kashin 240 na wutar lantarki zai shafa.

9. Duk da karin kudin wutar lantarkin da aka yi, amma kwastomomi na fuskantar koma baya na samun wuta tun daga watan Janairu 2024, wanda ministan wutar lantarki, Adebayo Adelabu ya danganta lamarin da karancin gas da ake fama da shi a kasar nan.

Sai dai wannan kari na kudin wutar lantarki da gwamnati ta yi, zai ta’allaka ne gaba daya da wutar da kwastomomi ke samu a rana, wanda da shi ne kadai za a yi alkalacin abin da za su biya duk wata.

10. Wadanda suke kan rukunin ‘A’ za a iya dawo da su wani rukunin matukar ba sa samun wutar lantarkin awa 20 a kowace rana.

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Bloomberg: Damuwa Game Da Karfin Sin Wajen Samar Da Hajoji Ba Ta Da Tushe

Bloomberg: Damuwa Game Da Karfin Sin Wajen Samar Da Hajoji Ba Ta Da Tushe

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.