ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Dukufa Magance Matsalolin Bangaren Lantarki, In Ji Minista

by Khalid Idris Doya
2 years ago
lantarki

Gwamnatin tarayya ta ce ta dukufa wajen ganin ta shawo kan asalin matsalolin da suke addabar bangaren wutar lantarki tare da nemo mafita a kansu.

Ministan wutan lantarki, Adebayo Adelabu shi ne ya shaida hakan a lokacin da ke ganawa da ‘yan jarida jim kadan bayan ganawa da ya yi da wasu masu ruwa da tsakani na jam’iyyar APC a sakateriyar jam’iyyar na Jihar Oyo da ke Oke-Ado a Ibadan.

  • Abubuwa 10 Da Ya Kamata A Sani Game Da Sabon Tsarin Biyan Kudin Wutar Lantarki
  • Matsanancin Rashin Lantarki Ya Addabi ‘Yan Nijeriya

Ministan ya ce Shugaban kasa, Bola Tinubu ya himmatu wajen kawo gagarumin sauyi a bangaren wutar lantarki.

ADVERTISEMENT

Ya ce, “Bari na yi amfani da wannan damar na tabbatar wa al’ummar Nijeriya cewa gwamnatin Bola Tinubu a shirye take wajen ganin ta sauya abubuwan da suke faruwa a harkar wutar lantarki, ta canja takun da ke bangaren. Wannan dalilin ne ya sa yanzu muka dukufa wajen shawo kan asalin matsalolin wutar lantarki.

“Muna yin wannan aikin shawo kan dukkanin matsalolin ne tare da yin aikin hadin guiwa da dukkanin masu ruwa da tsaki a bangaren domin nemo mafita, kama daga bangaren samar da gas zuwa tarawa, watsawa da kuma rarraba wutar lantarki hadi da su kansu kwastomomi masu amfani da lantarkin. Akwai abubuwa da dama da muke yi kuma abubuwa za su fara canzawa.”

LABARAI MASU NASABA

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

Ya ce a yanzu ma akwai ci gaba da ake samu a wasu wuraren, amma yanzu ma aka fara samun shawo kan lamura ta yadda ‘yan Nijeriya za su mori lantarki fiye da yadda suke tunani cikin rahusa da kuma inganci a wadace.

Adebayo ya roki ‘yan Nijeriya da su kara hakuri da gwamnatin Tinubu, yana mai cewa halin da ake ciki na wucin gadi ne lamura za su sauya nan ba da jimawa ba.

“Ni kaina na himmatu wajen ganin na shawo kan matsalolin da suke bangaren wutar lantarki, kuma tabbas a kwanan nan ‘yan Nijeriya za su fara rausayawa suna murna da ci gaba da za mu kawo a bangaren,” ya shaida.

Da yake magana kan kokarin gwamnati na shawo kan matsalar karancin mita a Nijeriya, ministan ya ce shugaban kasa ya kafa kwamitin kula da lamuran mita, kuma sun himmatu wajen samar da sama da biliyan 75 domin tabbatar da akalla mita guda miliyan 2 an sanyasu nan da shekaru biyar masu zuwa.

lantarki
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora

MASU ALAKA

lantarki
Labarai

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
lantarki
Labarai

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato
Manyan Labarai

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
Next Post
Kamfanonin Sin Sun Kara Kirkiro Sabbin Kayayyaki Masu Lambar Kira

Kamfanonin Sin Sun Kara Kirkiro Sabbin Kayayyaki Masu Lambar Kira

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026
lantarki

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
lantarki

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.