• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Majalisa 60 Sun Yi Barazanar Ficewa Daga PDP

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
‘Yan Majalisa 60 Sun Yi Barazanar Ficewa Daga PDP
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Akwai dai takun saka a babbar jam’iyyar adawa ta PDP, biyo bayan barazanar ficewa daga jam’iyyar da ‘yan majalisar tarayya kusan 60 suka yi kan zargin jam’iyyar APC mai mulki ne ke kulawa da kwamitin gudanarwa na jam’iyyar PDP.

Barazanar ‘yan majalisar dai ya biyo bayan nadin kwamitocin rikon kwarya na jam’iyyar PDP a Ribas da wasu jihohin kasar nan, wanda kwamitin gudanarwa na jam’iyyar karkashin jagorancin Umar Damagum ya yi.

  • Liu Yuxi Ya Halarci Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kan Sin Da Afirka Karo Na Uku
  • Yawan Motocin Da Sin Ta Sayar Ya Kai Miliyan 6.72 A Rubu’in Farkon Bana

A yayin wani taron manema labarai a Abuja, ‘yan majalisan sun bukaci a tsige Damagum daga mukaminsa na rikon kwarya na shugaban jam’iyyar PDP na kasa, inda suka yi gargadin cewa idan ba a yi haka ba, za su fice daga jam’iyyar.

Da suke magana kan zargin, masu magana da yawun gamayyar ‘yan majalisan dokokin na PDP, Hon. Ikenga Imo Ugochinyere, Hon. Aliyu Mustapha (Kaduna), Hon. Awaji-Inombek Abiante (Ribas), Hon. Midala Balami (Borno) da wasu da dama, sun yi watsi da matakin mukaddashin shugaban jam’iyyar PDP na kasa, na neman murkushe magoya bayan PDP tare da fifita ‘yan jam’iyyar APC, musamman a Jihar Ribas.

A cewar ‘yan majalisan, za su taimaka wa mukaddashin shugaban wanda yake rike da mukamin ba bisa ka’ida ba, wajen ruguza jam’iyyar PDP idan har bai janye matakin ba tare da duba jerin sunayen kwamitocin riko na Jihar Ribas da sauran jihohi 16.

Labarai Masu Nasaba

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

‘Yan majalisan sun kuma yi kira ga Damagum da ya yi murabus daga mukaminsa cikin gaggawa don ba da damar wani daga shiyyar Arewa ta tsakiya ya maye gurbinsa na kulawa da al’amuran jam’iyyar PDP bisa bin tsarin doka na ganin wani daga yankin Arewa ta tsakiya ya gaji tsohon shugaban jam’iyyar na kasa, Sanata Iyorchia Ayu da ya fito daga Jihar Benuwai, wanda aka tsige shi a ranar 28 ga Maris, 2023.

Sun sha alwashin taimaka wa Damagum wajen ruguza PDP idan ya ki cire ‘yan APC daga mambobin kwamitin riko na PDP a Ribas da wasu jihohi 16.

‘Yan majalisan sun dai zargi Damagun da nada ‘ya’yan jam’iyyar APC a cikin kwamitin riko na PDP na kananan hukumomi a Jihar Ribas da wasu jihohi da dama. Sun ce wannan mataki na iya kashe jam’iyyar PDP.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

APC Da PDP, Duk Kanwar Ja Ce -Kwankwaso

Next Post

Sin Na Adawa Da Amurka Da Ta Girke Makamai Masu Linzami A Yankin Asiya-Pasifik

Related

Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

1 week ago
‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

1 week ago
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Idan Kana Son Tarwatsa PDP, To Ka Dawo Da Peter Obi – Wike

1 week ago
ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro

2 weeks ago
katin zabe
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Bayyana Damuwarta Kan Katunan Zabe 360,000 Da Ba A Karba Ba A Kano

2 weeks ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

Shugabannin PDP Sun Shiga Dimuwa Yayin Da APC Ke Zawarcin Wasu Gwamnoninsu

2 weeks ago
Next Post
Sin Na Adawa Da Amurka Da Ta Girke Makamai Masu Linzami A Yankin Asiya-Pasifik

Sin Na Adawa Da Amurka Da Ta Girke Makamai Masu Linzami A Yankin Asiya-Pasifik

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

September 13, 2025
PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

September 13, 2025
Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

September 13, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

September 13, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

September 13, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido Ba

September 13, 2025
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

September 12, 2025
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.