• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharhi: Bukatar Sake Farfado Da Kiwon Tarwada A Nijeriya

by Abubakar Abba
1 year ago
in Noma Da Kiwo
0
An Rufe Rabin Masana’antun Kiwon Kifi A Jihar Filato
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kullum, bukatar kifin Tarwada kara karuwa yake a Nijeriya, duba da irin muhimmancin da yake da shi wajen gina jikin Dan Adam tare kuma da kara bunkasa tattalin arzikin wannan kasa.

Sai dai, akwai kalubale wajen kiwon Tarwadar, koda-yake amfani da dabarun kimiyyar zamani da kasuwanci, za su taimaka wajen samar da makoma mai dorewa a wannan fanni tare damammaki masu yawan gaske ga masu yin kiwon ta.

  • Ta Hanyar Tinkarar Wannan Muhimmin Batu Ne Kawai Za A Iya Inganta Dangantakar Dake Tsakanin Sin Da Amurka
  • Hajjin Bana: NAHCON Ta Ba Jihohi Wa’adin Mika Sunaye Maniyyata

Har ila yau, a Nijeriya an jima ana kiwon Tarwada a gargajiyance, wanda akasarin masu yin wannan kiwo; masu karamin karfi ne, sannan ba sa iya samun kayan kiwo na zamanin tare da dabarun kiwon, don samun kasuwar da ta dace.

Hakan ya yi sanadiyyar samun karancin Tarwadar da kuma rashin samun kudaden shiga masu yawa, rashin sarrafa ta yadda ya dace da kuma rashin samar da kayan aikin adana ta, wanda hakan kan jawo wa masu sana’ar yin asara a wasu lokutan.

Duk da wadannan kalubale, har yanzu fannin na samar da damammaki da suka hada da raguwar talauci, samar da ayyukan yi da kuma kara samar da wadataccen abinci a fadin wannan kasa.

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

Hikimar Yunƙurin Sake Farfaɗo Da Noman Filanten A Jihar Nasarawa

Baya ga kasancewar Nijeriya a matsayin kasa mafi yawan al’umma a Afirka, ta kuma kasance kan gaba a duniya wajen samar da wannan kifi na Tarwada, wanda aka kiyasta cewa; tana iya samar da Tarwada tan miliyan daya a shekarar 2021, wanda kudinta ya kai kimanin dala biliyan 2.6.

Haka zalika, a Nijeriya akwai matakai da dama da ake bi na kiwonta, domin samun wadatacciyar riba da suka hada da; kiwonta, sarrafa ta, kasuwancinta da yin amfani da ita da sauran makamantansu.

Don haka, kowane mataki daya daga cikin wadannan matakai, na da irin nasa kalubalen da kuma damammaki.

Bisa wani bincike da aka yi karkashin aikin kiwon Kifi na ‘FISH4ACP’, wanda ma’aikatar aikin noma da raya karkara ta gudanar ya nuna cewa, Nijeriya na da akalla masu samar da Tarwada kimanin 285,000, inda kananan masu kiwon suka doshi kashi 60 cikin 100.

Bisa hadaka a tsakanin hukumar abinci ta duniya (FAO) da ma’aikatar noma da raya karkara ta yi a kwanakin baya, sun kaddamar da wanzar da kashin farko na bunkasa kiwon Tarwada; don samun gwaggwabar riba a Nijeriya.

A yanzu haka, Nahiyar Turai (EU), da kuma ma’aiktar bunkasa tattalin arziki ne ke tallafa wa wannan aiki na ‘Fish4ACP’ a Nijeriya.

Kazalika, wannan wani shiri ne wanda kungiyar Afirka da jihohin da ke bakin teku (OCAPS), suka kirkiro da shi domin bayar da nasu goyon bayan wajen samar da wadataccen abinci mai gina jiki, kara habaka tattalin arziki da samar da ayyukan yi, samar da damar kasuwanci da zuba jari da kuma karfafa yin gasa a wannan fanni.

A nasa jawabin yayin kaddamar da shirin a Abuja, wakilin hukumar FAO a Nijeriya; Fred Kafeero ya bayyana cewa, aikin zai taimaka wajen farfado da fannin kiwon Tarwada a Nijeriya tare da samar da abinci da kuma habaka tattalin arzikin ‘ya’yan wannan kasa baki-daya.

Kafeero ya kara da cewa, Nijeriya na da matukar muhimmanci da dabaru a cikin sauran kasashe, wajen bunkasa kiwon Tarwada da kuma habaka kiwonta, don samun riba mai yawan gaske.

Wata tawagar Nahiyar Turai (EU), ta kawo ziyara kasar nan domin taimaka wa da dabarun kiwonta, musamman domin lalubo da mafita kan kalubalen da masu sana’ar da kuma ‘yan kasuwa ke fuskanta a Nijeriya.

Frank Okafor ne ya jagoranci tawagar a wajen taron, wanda ya ce, kungiyar ta mayar da hankali ne domin taimaka wa Nijeriya da sauran kasashen da ke Afirka, don samun damar cimma muradunsu ta hanyar taimaka wa da kudade tare da samar da dabarun cin nasara a wannan fanni na kiwonta a dukkanin fadin Afirka.

Shi kuwa Babban Sakatare a Mai’aikatar Aikin Noma da Raya Karkara, Dakta Ernest Umakhihe cewa ya yi, ma’aikatar ta mayar da hankali ne, don habaka kiwonta wanda ake sa ran za a kara samar da yawanta, domin samun wadatuwa da ta kai kimanin tan 250,000, don cimma bukatar da ake da ita a kasar tare da rage dogaron da ake da shi na shigo da ita daga kasashen ketare.

Bugu da kari, kara fafado da wannan fannin a Nijeriya, abu ne da ke bukatar hada karfi da karfe a tsakanin gwamnati, masu ruwa da tsaki, masu kiwonta, masu yin bincike da kuma masana’antu masu zaman kansu.

Kazalika, yin amfai da dabarun da suka kamata da kuma samar da dauki ga fannin, masana’antar kiwonta za ta iya bayar da gudunmawa wajen kara habakawa tare da bunkasa tattalin arzikin Nijeriya.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Jihar Bauchi Ta Yi Fintikau Wajen Aiwatar Da Shirin Noma Na Bankin Duniya – Dr. Kabir

Next Post

Jihar Oyo Na Horar Da Malaman Gona Domin Samun Wadatar Abinci

Related

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Noma Da Kiwo

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

6 days ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Noma Da Kiwo

Hikimar Yunƙurin Sake Farfaɗo Da Noman Filanten A Jihar Nasarawa

6 days ago
Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 
Noma Da Kiwo

Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 

7 days ago
Kin Biyan Bashi Daga Wasu Manoma Zai Kawo Cikas Ga Noman Shinkafa A Bana – Ɗan Madamin Samaru 
Noma Da Kiwo

Kin Biyan Bashi Daga Wasu Manoma Zai Kawo Cikas Ga Noman Shinkafa A Bana – Ɗan Madamin Samaru 

1 week ago
Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA
Noma Da Kiwo

Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA

2 weeks ago
Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025
Noma Da Kiwo

Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025

2 weeks ago
Next Post
Jihar Oyo Na Horar Da Malaman Gona Domin Samun Wadatar Abinci

Jihar Oyo Na Horar Da Malaman Gona Domin Samun Wadatar Abinci

LABARAI MASU NASABA

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

June 28, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Ƙoƙarin Ƙungiyoyin Afrika A Gasar Kofin Duniya

June 28, 2025
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

June 28, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

June 28, 2025
Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

June 28, 2025
Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

June 28, 2025
Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

June 28, 2025
Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

June 28, 2025
Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

June 28, 2025
Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.