• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ranar Ma’aikata Ta Bana: Albashin Naira 615,000 Muke Bukata Don Mu Rayu – ‘Yan Kwadago

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
ranar ma'aikata

Da alama har yanzu tsugune ba ta kare ba duk da karin albashin da Gwamnatin Tarayya ta sanar da kashi 25 zuwa kashi 35 ga ma’aikatanta, ana jajebirin bikin ranar ma’aikata ta shekarar 2024, yayin da Shuga-ban Kungiyar Kwadago ta Kasa (NLC), Kwamared Joe Ajaero ya bayyana cewa karin da gwamati ta ce ta yi ba zai yi wani tasiri bai dan aka duba halin da kasar take ciki a yanzu.

Kwamared Ajero wanda ya yi bayanin haka a ranar Laraba a wani shirin gidan talabijin na Chan-nels, ya bayyana cewa, su babban abin da suke so shi ne gwamnati ta yi musu karin kudin da zai ishi ma’aikaci ya rayu a kasar nan ba kawai karin da zai ci gaba da tsunduma shi a cin bashi ba kullum.

  • Ranar Ma’aikata: Bayan Cike Giɓin Albashin Da Muka Gada, Za Mu Ci Gaba Da Inganta Walwalar Ma’aikata – Gwamnan Zamfara
  • Ranar Ma’aikata: Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranar Laraba A Matsayin Hutu

“Mu abin da muke bukata shi ne albashin da za a iya biyan ma’aikaci yar ayu a Nijeriya. Kuma akalla shi ne a biya shi Naira 615,000. Kuma wannan ma a lissafin da muka yi ne kafin abubuwa su kara tsada irin na kwanan nan. Daga ciki a wata akalla ma’aikaci zai iya kashe Naira 110,000 a kan sufuri kawai, kudin wuta Naira 20,000 (wannan ma kafin a sanar da karin kudin wutar da aka yi kwanan baya ne). Sannan ma’aikacin da yake da akalla iyali mutum shida zai iya kashe Naira 50,000 a kiwon lafiya, shi ma idan babu tiyata ko wata lalaurar rashin lafiya da za ta ci kudi sosai. Haka nan kudin haya, ma’aikaci na bukatar biyan akalla Naira 40,000 duk wata, haka nan yana bukatar akalla Naira 20,000 na sayen fetur da kananzir a wata, ga batun abinci da kudin makaran-ta da kayan marmari da sauransu. Duka idan aka hada lissafi ya kamata a biya ma’aikaci Naira 615,000 don ya iya rayuwa a Nijeriya. Wanda bai amince da hakan ba kuma zai iya zuwa kasuwa da kansa ya yi safiyon kudaden abubuwan da muka ambata.” Ya bayyana.

Shugaban ‘yan kwadagon ya kuma yi nuni da cewa karin albashi don ya dace da yanayin da ake ciki a kasa abu ne da ake yi a duk fadin duniya, don haka bai kamata gwamnatin Nijeriya ta zama daban a cikin dangi ba, inda ya yi kira ga ma’aikata su kara jajircewa wajen cimma nasarar abubuwan da suka tasa a gaba na ganin an inganta walwalarsu.

A ranar Talata da dare ne dai, Gwamnatin Tarayya ta sanar da karin albashi da kashi 25 zuwa 35 ga ma’aikatanta wanda ta ce zai fara aiki tun daga ranar 1 ga Janairun 2024. Abin da ya rage dai yanzu shi ne lokacin da gwamnatin za ta biya bashin albashin da kuma dorewa da biyan karin, kasancewar har yanzu akwai masu bin bashin alawus na Naira 35,000 da ta ce za ta ba kowane ma’aikaci don rage radad-in cire tallafin maid aga watan Satumbar 2023.

LABARAI MASU NASABA

An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa
Kotu Da Ɗansanda

An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

November 8, 2025
An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi
Kotu Da Ɗansanda

An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

November 8, 2025
Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma
Manyan Labarai

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
Next Post
Jamb

Matsalolin Da Hukumar JAMB Ta Fuskanta A Jarrabawar Bana

LABARAI MASU NASABA

An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

November 8, 2025
An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

November 8, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025
Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.