• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mu Kare Daraja Muhallinmu, Kuma Mu Kare Nijeriya Daga Labaran Bogi – Minista

by Sulaiman
1 year ago
Minista

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana cewa kafafen yaɗa labarai wani babban ginshiƙi ne na haɓaka muhalli tare da kare martabar mulkin dimokiraɗiyya.

Ministan ya faɗi haka ne a lokacin bikin ba shi lambar yabo a wani ɓangare na Ranar ‘Yancin Aikin Jarida wanda aka yi a Abuja.

  • Gwamnatin Katsina Ta Ɗauki Ma’aikata 304 Don Kula Da Zirga-zirgar Ababen Hawa A Jihar
  • An Bukaci Manoma Su Kara Yawan Kwakwar Manjan Da Suke Nomawa

Ƙungiyar ‘Yan Jarida ta Nijeriya (NUJ) ita ce ta karrama shi da lambar.

A jawabin sa jim kaɗan bayan ya karɓi lambar, Idris ya bayyana farin ciki da karramawar, musamman ganin ayyukan da ya yi da muƙaman da ya riƙe a fagen aikin jarida kafin a naɗa shi minista.

Ya ce: “Wannan karramawa ta yi min sosai, wanda ke da muhimmanci a kai na da kuma gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, GCFR.

LABARAI MASU NASABA

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

“Wannan kyakkyawan karimcin zai zaburar da ni na sake sadaukar da kai ga hidimar al’ummar mu mai girma da kuma bil’adama baki ɗaya.”

Da yake magana kan taken bana na Ranar ‘Yancin Aikin Jarida, wato “Jarida ta Duniya: Aikin Jarida a Yayin da ake Fuskantar Matsalar Muhalli,” sai ministan ya ce, “A yayin da ake fuskantar matsalar muhalli, ’yan jarida sun kasance masu kula da gaskiya da kuma masu fafutikar tabbatar da gaskiya. Suna ƙarin haske kan rashin adalci na muhalli, suna fallasa ayyukan da ba daidai ba, da kuma ɗaga muryar waɗanda lalacewar muhalli ta fi shafa. Ta hanyar rahoton binciken su, suna ɗaukar gwamnatoci da ƙungiyoyin kamfanoni alhakin ayyukan su da bayar da shawarar manufofin da ke haɓaka ɗorewa da kiyaye duniyar mu.

“Taken taron na bana ya yi tasiri sosai kan manufofin ma’aikatar mu da kuma batutuwan da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sa a gaba, waɗanda suka haɗa da maido da amana, sake daidaita ƙimar ƙasa, da samar da yanayi mai kyau ga kafafen yaɗa labarai. Ya jaddada muhimmancin aikin jarida wajen magance matsalar muhalli.”

Ya ƙara da cewa, “A cikin tarihi, kafofin watsa labarai, a matsayin masu kula da gaskiya kuma masu samar da sauyi na zamantakewa, sun yi tsayin daka don yin la’akari, suna shawagi a kan ayyukan mutane, gwamnatoci, da kamfanoni.

“A wannan lokaci na rikicin muhalli, aikin watsa labarai ya wuce bayar da rahoto kawai; ya na ƙunshe ne da sadaukar da kai don shirya ayyukan gama-gari don amfanin jama’a. Tare da ikon faɗakarwa, ilmantarwa, da zaburarwa, kafofin watsa labarai su na da ikon da ba zai misaltu ba don kunna motsi, ɗaukaka muryoyi, da haifar da canjin ɗabi’a ga muhalli.”

Bugu da ƙari, Idris ya ce, “Yayin da mu ke bikin Ranar ‘Yancin ‘Yan Jarida ta Duniya, dole ne mu yi tunani a kan muhimmancin kafafen watsa labarai masu ‘yanci don bunƙasa mulkin dimokiraɗiyya, inganta gaskiya, da kuma kare haƙƙin bil’adama.

“Aikin jarida ya zama ginshiƙin tsarin dimokiraɗiyya ta hanyar samar da muhimmin dandali na yaɗa labarai, musayar ra’ayi, da kuma ɗora wa masu riƙe da madafun iko alhakin su.

“Kafafen yaɗa labarai na Nijeriya sun kasance masu fafutikar tabbatar da ɗorewar mulkin dimokiraɗiyya a ƙasar nan, kuma a irin wannan lokaci, mu na jinjina wa jajircewa da sadaukarwar ku kan aikin jarida.

“Duk da haka, yayin da mu ke murnar gudunmawar da ‘yan jarida ke bayarwa ga al’umma, mun kuma yarda da ƙalubalen da ‘yan jarida ke fuskanta wajen gudanar da muhimman ayyukan su. A matsayin su na masu kare muhalli, ‘yan jarida su kan fuskanci barazana, tsangwama, da tashin hankali saboda jajircewar su wajen fallasa laifukan muhalli da kare duniyar mu.”

Dangane da Ranar ‘Yancin ‘Yan Jarida ta Duniya, ministan ya ce dole ne mu sake jaddada aniyar mu ta kare haƙƙin ‘yan jarida da tabbatar da tsaron su.

“A matsayi na na Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, ina so in ƙara jaddada aniyar mu ta kare ‘yancin aikin jarida, inganta ra’ayoyi mabambanta, da kare haƙƙin ‘yan jarida.

“Mu ƙara zage damtse wajen gina makoma inda aikin jarida zai bunƙasa, a tabbatar da ‘yancin ‘yan jarida, da kuma kare duniyar mu har zuwa al’ummomi masu zuwa.

“Yayin da mu ke gudanar da ayyukan mu, dole ne mu kuma tuna cewa Nijeriya, muhallin mu, ita ce abin da ya kamata mu fara karewa daga labaran ƙarya.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
Manyan Labarai

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

November 1, 2025
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

November 1, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

November 1, 2025
Next Post
Xi Ya Yi Tattaunawa Da Macron

Xi Ya Yi Tattaunawa Da Macron

LABARAI MASU NASABA

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

November 1, 2025
Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

November 1, 2025
Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar

November 1, 2025
Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

November 1, 2025
Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

November 1, 2025
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

November 1, 2025
Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?

Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?

November 1, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

November 1, 2025
Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

November 1, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.