• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wutar Lantarki Ta Yi Ajalin Wani Mutum A Bayelsa

by Sadiq
1 year ago
in Labarai
0
Wutar Lantarki Ta Yi Ajalin Wani Mutum A Bayelsa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani mutum mai suna Amas ya rasa ransa sakamakon makalewa da ya yi a jikin wayar wutar lantarki a unguwar Ekeki, kusa da hedikwatar ‘yansanda da ke kan titin Azikoro a Yenagoa, babban birnin Jihar Bayelsa.

Marigayin dai ba ma’aikacin Kamfanin Power Holding Company of Nigeria (PHCN) ba ne, amma yana zaune ne a unguwar kuma yana hada wa mutane wuta.

  • 2027: Ganawar Manyan Jam’iyyun Adawa Ta Kara Wa Yunkurin Maja Kaimi
  • CAC Da Masu POS Sun Amince Da Wa’adin Mako Biyu Don Rijista

Mazauna yankin sun shaida wa manema labarai cewa, sakamakon rashin wutar lantarki da ake fama da shi a jihar, akasarin mutane sun gwammace hada wutar lantarki a kan layin gwamnatin tarayya wanda ake samun wutar lantarkin akalla sa’o’i 12 zuwa 13 a kullum.

Marigayin dan asalin karamar hukumar Nembe a jihar ya rasu ya bar ‘ya’ya biyu, ya makale ne a kan wayar wutar lantarkin kafin jami’an kamfanin PHCN su sauko da shi.

Wani mazaunin Azikoro mai suna Micheal Orubo wanda lamarin ya faru a kan idonsa, ya bayyana marigayin a matsayin mutum mai saukin kai wanda yake aikin hada wutar lantarki domin kula da iyalinsa.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

Ya ce, “Amas yana zaune a unguwarmu, kuma yana aikin hada wuta ne a yanki. Me ya sa mutuwa za ta zo masa a haka? Ya tafi ya bar mu ba zai sake dawowa ba.

“Yana da saukin kai, wa zai kula da yaran da ya bari. Kudin da yake samu a aikin hada wutar lantarki da shi yake amfani wajen ciyar da iyalinsa. Wace irin mutuwa ce wannan? Mutumin da muke tare tsawon lokacin da ake ruwan sama yanzu, ya tafi ne da nufin idan ruwa ya dauke ya gyara musu wuta.”

Wani mazaunin yankin ya ce, “Ya wuce ni bai wuce minti biyar ba. Ruwan sama yana tsayawa, sai ihun mutane muka jiyo, nan take muka garzaya wajen da lamarin ya faru amma ba za mu iya taimakonsa ba, saboda ya daure jikinsa da bel, don haka ya makale sosai a jikin falwaya, saboda duk mun tsorata kuma har yanzu ana ruwan sama.”

Ma’aikatan kamfanin wuta na PHCN, daga baya sun zo sauke gawar daga jikin falwayar da ya makale.

Kakakin rundunar ‘yansandan jihar, ASP Musa Muhammed bai ce komai kan faruwar lamarin ba zuwa lokacin hada wannan rahoton.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AjaliBayelsaFalwayaWutar Lantarki
ShareTweetSendShare
Previous Post

2027: Ganawar Manyan Jam’iyyun Adawa Ta Kara Wa Yunkurin Maja Kaimi

Next Post

RA’AYI: Sauye-sauyen Sheka Ba Zai Sa Ka Ci Zabe Ba A Nijeriya

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

2 hours ago
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna
Labarai

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

3 hours ago
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu
Manyan Labarai

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

4 hours ago
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya
Labarai

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

5 hours ago
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF
Manyan Labarai

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

7 hours ago
Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike
Manyan Labarai

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

9 hours ago
Next Post
RA’AYI: Sauye-sauyen Sheka Ba Zai Sa Ka Ci Zabe Ba A Nijeriya

RA’AYI: Sauye-sauyen Sheka Ba Zai Sa Ka Ci Zabe Ba A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.