• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Guguwa Mai Karfi Ta Yi Ajalin Mutum 4 A Kasuwar Baje Koli A Bauchi

by Khalid Idris Doya
1 year ago
Gwamna Bala

Wata mummunar guguwa da aka yi a daren ranar Asabar a cikin garin Bauchi ta janyo asarar rayukan mutum hudu a IBB Square inda ake gudanar da kasuwar baje kolin duniya ta arewa maso gabas.

Muhallin IBB square da ke Bauchi dai tsawon makonni ya karbi bakwancin kasuwar baje koli na shiyyar arewa maso gabas inda jihohin da ke shiyyar suka halarta. Guguwar ta yi barna a rumfunan jihar Gombe da Yobe, da kuma tantunan kasuwanci daban-daban da suke cikin kasuwar.

  • Sanata Saliu Ya Raba Taki Da Injinan Ban Ruwa Ga Manoman Kwara
  • Kwamishinan Bauchi Ya Rasu A Hatsarin Mota

A kokarin aikin ceto da ‘yansanda da sauran jami’ai suka yi, sun shiga tantuna da rumfuna domin lalubo wadanda tsautsayin ya rutsa da su inda suka kwashi wadanda suka gamu da barnar zuwa asibiti domin neman kulawar gaggawa na likita.

Da ya ke tabbatar da faruwar lamarin a ranar Lahadi, kakakin rundunar ‘yansanda a jihar Bauchi, SP Ahmad Muhammad Wakil, ya ce, mutum biyar ne aka samu a cikin gine-ginen da suka rufta din, inda hudu daga cikinsu suka rasa rayukansu.

Wadanda suka rasa rayukansu din su ne Abdullahi Abubakar, dan shekara 38 da ke unguwar Yakubu Wanka, Sadiq Ahmed Alfa, mai shekara 32 mazaunin unguwar Fadaman Mada, Malam Musa daga Maliya Ventures, Tudun Salmanu da kuma Abdullahi Abdurrahman wanda ya fito daga jihar Gombe.

LABARAI MASU NASABA

ACF Ta Yi Zargin Shiri Na Musamman Don Rusa Matatar Man Dangote

Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

“Mace daya ce taf ta tsira daga cikin mutum 5 da hatsarin guguwar ta shafa wato Fatima Isa ‘yar shekara 31 da ta ke unguwar Inkil a cikin garin Bauchi, wacce a yanzu haka take amsar kulawar likitoci a asibiti.”

Hukumomi dai sun dukufa daukan matakan da suka dace ciki har da kai gawarwakin mamatan zuwa dakin adana gawarwaki da kuma bibiyar irin asarar da aka tafka sakamakon guguwar.

Tunin dai a cewar Wakil, ‘yansanda suka bazama wajen tabbatar da cewa bata-gari ba su yi amfani da wannan damar wajen yi wa ‘yan kasuwan baje kolin sata ba domin tabbatar da kare musu dukiya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Matatar dangote
Labarai

ACF Ta Yi Zargin Shiri Na Musamman Don Rusa Matatar Man Dangote

October 10, 2025
Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus
Labarai

Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

October 10, 2025
Gwamnatin Kogi Ta Yaba Wa Tinubu Kan Naɗin Amupitan Shugaban INEC
Labarai

Gwamnatin Kogi Ta Yaba Wa Tinubu Kan Naɗin Amupitan Shugaban INEC

October 10, 2025
Next Post
Ƴansanda Sun Daƙile Yunƙurin Kai Hari Gidan Shugaban Jam’iyyar APC Na Kano

Ƴansanda Sun Daƙile Yunƙurin Kai Hari Gidan Shugaban Jam'iyyar APC Na Kano

LABARAI MASU NASABA

Matatar dangote

ACF Ta Yi Zargin Shiri Na Musamman Don Rusa Matatar Man Dangote

October 10, 2025
Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

October 10, 2025
Gwamnatin Kogi Ta Yaba Wa Tinubu Kan Naɗin Amupitan Shugaban INEC

Gwamnatin Kogi Ta Yaba Wa Tinubu Kan Naɗin Amupitan Shugaban INEC

October 10, 2025
Annabi (SAW) Shi Ne Mai Girman Duk Wani Mai Girma Da Allah Ya Taɓa Yi (2)

Annabi (SAW) Shi Ne Mai Girman Duk Wani Mai Girma Da Allah Ya Taɓa Yi (2)

October 10, 2025
Arewa Ta Daina Zama Ci-Ma Zaune A Tattalin Arziƙi – Gwamnan Bauchi

Arewa Ta Daina Zama Ci-Ma Zaune A Tattalin Arziƙi – Gwamnan Bauchi

October 10, 2025
Cutar Kwalara Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuƙe

Cutar Kwalara Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuƙe

October 10, 2025
Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

October 10, 2025
An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

October 9, 2025
Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

October 9, 2025
‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

October 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.