• English
  • Business News
Sunday, August 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Na’urar Auna Yawan Masu Kallon Talabijin Ta Farko A Nijeriya

by Sulaiman
1 year ago
in Labarai
0
Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Na’urar Auna Yawan Masu Kallon Talabijin Ta Farko A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ƙaddamar da na’urar auna masu kallo domin samar da sahihin bayanai na masu kallon talabijin a ƙasar nan.

A cikin wata sanarwa da Rabiu Ibrahim, Mataimaki na Musamman kan Harkokin Yaɗa Labarai ga Ministan, Idris, wanda ya ƙaddamar da taron a Abuja a ranar Alhamis, ya ce na’urar tana da matuƙar muhimmanci wajen tabbatar da cewa ayyukan watsa shirye-shirye ba wai kawai suna da tasiri ba har ma suna nuna abubuwa daban-daban da masu sauraro suka fi so kuma suke buƙata.

  • Rikicin Sarautar Kano: Kallo Ya Sake Komawa Kotu
  • Kamfanin Google Ya Kaddamar Da Shirin Koyar Da Darasi 10 Kan Kirkirarriyar Basira

Ya ce: “Kayan aiki ne wanda ke ba mu ikon fahimta da kuma ba da amsa ga yanayin masu amfani da kafofin watsa labarai, samar da kyakkyawar fahimta a cikin halayen kallon su, da abubuwan da suka fi so.

“Don haka abin farin ciki ne a lura cewa a ƙarshe an samu nasara a wannan aikin da aka fara a shekarar 2020.”

Ministan ya bayyana ɓullo da na’urar a matsayin wani gagarumin cigaba da ya yi daidai da manufar Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu na ganin Nijeriya ta samu cigaba da bunƙasar fasaha.

Labarai Masu Nasaba

Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho

Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata

Ya ce ɓullo da na’urar ya zama dole sosai domin har yanzu Ma’aunin Masu Kallo ko Sauraro na yin amfani da tsohon tsarin Alƙalamin da Takarda na tattara bayanai kan masu kallon talabijin da masu sauraren rediyo, wanda hakan ba ya nuna haƙiƙanin abin da ko yawan mutanen da ke kallo ko sauraron wani shiri na musamman.

“Hakazalika, masu tashoshi, masu shirye-shirye, ‘yan wasa, ba su amfana ta hanyoyi da yawa; mafi muhimmanci, ba su da ƙwazo ko ƙalubalen samar da ƙarin shirye-shirye mafi kyau wanda ke biyan ‘buƙatu’, a matsayin ma’aunin wanda yake so, abin da yake so, yawan yadda yake so, da dai sauran su. Wannan ya hana ci gaban ɗaukacin harkokin nishaɗi da yaɗa labarai a Nijeriya.”

Ministan ya ce abin takaici ne ganin cewa duk da cewa ƙasar tana da yawan masu kallo sama da sau uku a Afirka ta Kudu, kuɗaɗen da ake samu a tallace-tallacen talabijin na Nijeriya ya yi kaɗan idan aka kwatanta shi da na ƙasar Afirka ta Kudu, da kuma Kenya, lamarin da ya sa dole a yi amfani da tsarin da zai tabbatar da cewa kuɗin da ake kashewa a tallace-tallace a Nijeriya ya ƙaru sosai cikin shekaru biyu masu zuwa.

Idris ya ce: “Ina da yaƙinin cewa Na’urar Auna Masu Sauraro na gaskiya kuma tabbatacce zai jawo hannun jari mai yawa a ɓangaren yaɗa labarai, da bunƙasa tattalin arziki da samar da ayyukan yi.

“Hakan kuma zai ƙara wa Nijeriya suna a matsayin kasuwa mai ingantacciyar hanyar nazarin kafafen yaɗa labarai.”

Idris ya ce aikin wanda zai samar da ayyukan yi 500 kai-tsaye da kuma ayyuka 2,500 a fakaice an tsara shi ne don da sake farfaɗo da harkar yaɗa labarai a Nijeriya da kuma inganta shi domin tunkarar zamani domin har yanzu Gwamnatin Tarayya na kan hanyar aiwatar da Canji zuwa Dijital.

Ya nanata ƙudirin Shugaba Tinubu na bunƙasa harkar yaɗa labarai gaba ɗaya a Nijeriya kamar yadda ya bayyana a cikin umarnin da ya ba Ma’aikatar Masana’antu, Kasuwanci da Saka Hannun Jari ta Tarayya da Bankin Masana’antu a kwanan baya na faɗaɗa hanyoyin hada-hadar kuɗi ga Masana’antar Watsa Labarai.

Ministan ya umarci mai ba da sabis, First Media Entertainment Integrated Limited/GARB, ya haɓaka faɗakarwar jama’a da ba da shawarwari ga duk ƙungiyoyin sashe waɗanda suka dace don yin amfani da isassun damar Na’urar Auna Masu Kallo.

Taron ya samu halartar Ministar Fasaha, Al’adu da Tattalin Arzikin Ƙirƙire-ƙirƙire, Barista Hannatu Musawa; Shugabar Kwamitin Yaɗa Labarai na Majalisar Dattawa; Shugaban Kwamitin Majalisar Dattawa kan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Sanata Eze Kenneth Emeka; Shugaban Kwamitin Majalisar kan Yaɗa Labarai, Wayar da Kai, Ɗa’a da Ɗabi’u na Ƙasa, Hon. Steve Fatoba; Jakaden Bulgeriya a Nijeriya, Yanko Yordanov; tsohon Ministan Yaɗa Labarai, Alhaji Lai Mohammed; Mai ba Shugaban Ƙasa Shawara na Musamman kan Yaɗa Labarai da Dabaru, Mista Bayo Onanuga, da dukkan manyan daraktocin hukumomi a ma’aikatar da sauran manyan baƙi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan makarantaArtvNTA
ShareTweetSendShare
Previous Post

Rikicin Sarautar Kano: Kallo Ya Sake Komawa Kotu

Next Post

Sharhin Littafin Zube Na ‘Sidi Ya Shiga Makaranta’ Na Umaru Ladan Da Michael Crowder (1)

Related

Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho
Labarai

Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho

36 minutes ago
Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata
Labarai

Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata

2 hours ago
NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja
Manyan Labarai

NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja

3 hours ago
Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto
Labarai

Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

16 hours ago
An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja
Manyan Labarai

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

21 hours ago
Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi
Labarai

Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

22 hours ago
Next Post
Sharhin Littafin Zube Na ‘Sidi Ya Shiga Makaranta’ Na Umaru Ladan Da Michael Crowder (1)

Sharhin Littafin Zube Na ‘Sidi Ya Shiga Makaranta’ Na Umaru Ladan Da Michael Crowder (1)

LABARAI MASU NASABA

Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho

Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho

August 10, 2025
Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata

Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata

August 10, 2025
NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja

NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja

August 10, 2025
Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa

Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa

August 10, 2025
Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

August 10, 2025
Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

August 9, 2025
Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

August 9, 2025
Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

August 9, 2025
Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

August 9, 2025
Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

August 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.