• English
  • Business News
Friday, September 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gudunmawa 10 Da Ilimi Ke Bayarwa Ga Al’umma (2)

by Idris Aliyu Daudawa
1 year ago
in Ilimi
0
Gudunmawa 10 Da Ilimi Ke Bayarwa Ga Al’umma (2)
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kowane lokaci, ilimi na samun tagomashi da kuma girmamawa daga wurin al’umma. Masu ilimi, su ne ke samun ingantacciyar rayuwa, wadda kowa da kowa ke sha’awa ko mararin samun irin ta.

Idan mutane suka karanci bangaren fannonin da ake ribibin su wajen daukar ma’aikata, ko shakka babu suna samun albashi mai matukar tsoka, ta yadda za su taimaki kansu da iyayensu da sauran danginsu baki-daya.

  • Gudunmawa 10 Da Ilimi Ke Bayarwa Ga Al’umma
  • Gwamna Yusuf Zai Ayyana Dokar Ta-ɓaci A Fannin Ilimi A Kano

Har ila yau, ilimi na sa a samu daukaka; wadda ba a taba zato ba, sannan yana taimakawa wajen cimma kowane irin buri na rayuwa.

Bugu da kari, ilimi na bayar da dama wajen samun kudaden da za su taimaka wa mutum a rayuwarsa ta yau da kullum tare kuma da samun farin ciki ta fuskoki daban-daban.

6- Masu Ilimi Na Matukar Taimaka Wa Al’umma 

Labarai Masu Nasaba

Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME

Malaman Jami’o’i Sun Zama Abin Tausayi —Kungiyar ASUU

Ta wace hanya masu ilimi ke taimaka wa al’umma? Kasancewar masu ilimi, sun san muhimmancinsa tare kuma da sanin abin da ya kamata, shi yasa a duk inda suka fi yawa ake samun zaman lafiya da hadin kai da kuma rayuwa mai inganci.

Haka nan, abu ne mai dadi mutum ya kasance cikin al’umma, wadda ta san martaba da taimakon junanta tare da kai wajen ciyar da al’umma baki-daya gaba.

Sannan, a duk wurin da masu ilimi ke da rinjaye, suna kokarin taimaka wa masu karamin karfi, musamman ta bangarorin da suka gaza, don su ma su samu farin ciki da walwala a tasu rayuwar.

7- Samar Da Al’umma Mai Tafiya Daidai Da Zamani 

Ilimi shi ne babban jagoran ci gaban al’umma, don haka ya kamata mutum ya yi kokari ya san abubuwan da suka shafi al’adunsa, tarihi da kuma sauran al’amuran da suka shafe shi kai tsaye.

Haka zalika, a koda-yaushe ilimi na tafiya ne da zamani; shi yasa masu ilimi ba a taba barin su a baya, wajen rungumar sabbin abubuwan da zamani ke dauke da su.

Har ila yau, kamar yadda kowa ya sani ne cewa, ilimi haske ne; sannan kuma wata kofa ce ta fahimtar dukkanin wasu al’amuran rayuwa.

8- Mu’amala Daban-daban

Ilimin fasahar zamani, na taimakawa wajen hada mutane da kamfanoni daga ko’ina a fadin duniya ba tare da wata katanga ba, muddin dai za a iya yin mu’amala tare da yin musayar ra’ayi da mutane daga wasu kasashe masu al’adu mabambanta, wannan kai tsaye yana nuni ne da irin muhimmancin da ilimi yake da shi.

Sa’annan, ilimi yana matukar taimaka mana wajen sanin juna da yin mu’amala ta kai tsaye, duk kuwa da irin banbance-banbancen da ke tsakaninmu.

9- Samar Da Damar Taimakawa 

Gudunmawar da ilimi ke bayarwa a tsakanin al’umma, na da matukar yawa; duba da cewa, a irin wannan zamani babu wani abu da zai iya yiwuwa ba tare da ilimi ba.

Idan muka dubi bangaren shugabanci, sanin kowa; babu yadda za a yi jahili ya jagoranci al’umma, koda kuwa a Karkara ne; ballantana kuma a Birane.

Haka nan, batun kasuwanci a halin yanzu; musamman yadda duniya ta canja, kusan komai ya zama na ilimi. Don haka, da zarar ka kasance a matsayin jahili; akwai kasuwanci da dama da zai fi karfinka, sai dai ka zama dan kallo.

10- Daga Darajar Dan’adam

Ko shakka babu, babu abin da ke mayar da Dan’adam ya zama cikakken mutum; tamkar Ilimi, domin kuwa wani mabudi ne wanda ke mayar da mara karfi ya zama mai karfi, wanda ba dan kowa ba; ya zama ya gagara a tsakanin al’umma, sakamakon wannan ilimi da yake da shi.

Har ila yau, ilimi ne kadai zai mayar da dan talaka ya zama wani mashahurin malami ko mai mulki ko kuma wani mai fada a ji.

Hakan ya sha faruwa a tsakanin al’umma, domin kuwa ana samun shugaban kasa, gwamna, sanata, minista da sauran makamantansu, wanda dan talakawa ne kowa ya sani; amma darajar ilimi ta ba shi wannan daukaka.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: IlimiMakarantaSchool
ShareTweetSendShare
Previous Post

Bayan Rasa Kujerar Minista Da Wata 10, Shetti Ta Yi Aure

Next Post

Zartar Da Hukuncin Kisa Ya Karu A Duniya, In Ji Amnesty

Related

Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME
Ilimi

Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME

4 days ago
ASUU
Ilimi

Malaman Jami’o’i Sun Zama Abin Tausayi —Kungiyar ASUU

5 days ago
Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Da ɗumi-ɗuminsa

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

7 days ago
Lambar Yabo Ta CON: Buni Ya Zama Zinare Bashi Da Maboya
Ilimi

NTIC Ta Jinjina Wa Gwamna Buni Kan Taimako A Bangaren Ilimi

2 weeks ago
Hukumar SUBEB Ta Yi Kira Ga Al’umma Da Su Sa ‘Ya’yansu Makaranta
Ilimi

Hukumar SUBEB Ta Yi Kira Ga Al’umma Da Su Sa ‘Ya’yansu Makaranta

2 weeks ago
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

3 weeks ago
Next Post
Zartar Da Hukuncin Kisa Ya Karu A Duniya, In Ji Amnesty

Zartar Da Hukuncin Kisa Ya Karu A Duniya, In Ji Amnesty

LABARAI MASU NASABA

Tattalin Arzikin Sin Babban Ginshiki Ne Na Karuwar Tattalin Arzikin Duniya

Tattalin Arzikin Sin Babban Ginshiki Ne Na Karuwar Tattalin Arzikin Duniya

September 12, 2025
Duniya Za Ta Ci Karin Gajiya Daga Karfafuwar Hadin Gwiwar BRICS 

Duniya Za Ta Ci Karin Gajiya Daga Karfafuwar Hadin Gwiwar BRICS 

September 12, 2025
Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

September 11, 2025
Sin Ta Kasance Kan Gaba A Yawan Hakkin Mallakar Fasaha A Bangaren Tattalin Arziki Na Dijital

Sin Ta Kasance Kan Gaba A Yawan Hakkin Mallakar Fasaha A Bangaren Tattalin Arziki Na Dijital

September 11, 2025
Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki

Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki

September 11, 2025
Za A Gudanar Taron Tattaunawa Karo Na 12 Na Dandalin Xiangshan A Nan Birnin Beijing

Za A Gudanar Taron Tattaunawa Karo Na 12 Na Dandalin Xiangshan A Nan Birnin Beijing

September 11, 2025
Shettima

Shettima Ya Bada Umarnin Gaggauta Raba Lamunin Naira Biliyan 250 Ga Ƙananan Manoma 

September 11, 2025
An Zabi Wuraren Ban Ruwa Hudu Na Kasar Sin Domin Shigar Da Su Jadawalin Wuraren Ban Ruwa Na Kasa Da Kasa

An Zabi Wuraren Ban Ruwa Hudu Na Kasar Sin Domin Shigar Da Su Jadawalin Wuraren Ban Ruwa Na Kasa Da Kasa

September 11, 2025
Rashin Tsaro: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jihar Kogi 

Rashin Tsaro: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jihar Kogi 

September 11, 2025
Shawarar Jagorantar Harkokin Duniya: Mafitar Sin Ga Kasa Da Kasa

Shawarar Jagorantar Harkokin Duniya: Mafitar Sin Ga Kasa Da Kasa

September 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.