• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

 An Haramta Yi Wa Mata Kaciya A Gambiya

by Sadiq
11 months ago
in Kasashen Ketare
0
 An Haramta Yi Wa Mata Kaciya A Gambiya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

‘Yan majalisar dokokin kasar Gambiya, sun amince da wasu shawarwari wanda ya haramta yi wa mata kaciya, bayan da aka kada kuri’a a majalisar.

Tun a 2015 ne dai aka haramta yi wa mata kaciya a Gambiya, amma tsarin al’adar da ke da tushe ya ci gaba da yaduwa, kuma hukuncin farko da aka yanke a bara ya haifar da cece-kuce a kan dokar.

  • Tsoffin Shugabannin Sin Da Guinea Bissau Sun Taka Rawar Gani Wajen Kirkirar Zumunci Tsakanin Kasashen Biyu
  • Gwamnan Zamfara Ya Samu Lambar Yabo Kan Ƙirƙiro Ayyukan Ci Gaba

Bayan zazzafar muhawara a ranar Litinin, kudirin da ke kunshe cikin rahoton kwamitin hadin gwiwa na kiwon lafiya da jinsi ya zartas da cikakken zama a majalisar, inda ‘yan majalisa 35 suka kada kuri’ar amincewa da kudurin, yayin da 17 kuma suka ki amincewa, biyu kuma ba su kada kuri’a ba.

A halin yanzu an sanya ranar 24 ga watan Yuli, a mastayin ranar da za a yanke hukuncin ko za a sanya kaciyar nata a matsayin aikata laifi ko akasin haka.

Idan majalisar ta amince da hakan, Gambiya za ta zama kasa ta farko da ta janye dokar hana kaciya.

Labarai Masu Nasaba

Trump Ya Umarci A Bincika Lafiyar Ƙwaƙwalwar Tsohon Shugaban Ƙasa Biden Yayin Mulkinsa

Tawagar MDD Da Majalisar Shugabancin Libya Sun Kafa Kwamitin Tsagaita Bude Wuta

A watan Maris ne aka yi karatu na biyu inda ‘yan majalisa biyar daga cikin 53 suka kada kuri’ar kin amincewa da shi, daya kuma ya ki kada kuri’a.

Bayan karatu na biyu, kwamitin hadin gwiwa ya gudanar da taron tuntubar al’umma na kasa tare da shugabannin addini da na gargajiya, likitoci, wadanda abin ya shafa, kungiyoyin farar hula da masu kaciya da dai sauransu.

Sakamakon bincike da tuntubar da aka yi na nuni da cewa, duk nau’ikan yi wa mata kaciya cin zarafin mata ne da azabtarwa da kuma nuwawa mata wariya.

Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO), ta ce yi wa mata kaciya ba shi da wata fa’ida ga lafiya kuma yana iya haifar da zubar jini da yawa, firgita, matsalolin tunani har ma da mutuwa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DokaGambiyaHaramciKaciyaMata
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kura Ta Tsere Daga Kejinta A Jos

Next Post

Tinubu Ya Taya Sheikh Dahiru Bauchi Murnar Cika Shekaru 100

Related

Trump Ya Umarci A Bincika Lafiyar Ƙwaƙwalwar Tsohon Shugaban Ƙasa Biden Yayin Mulkinsa
Kasashen Ketare

Trump Ya Umarci A Bincika Lafiyar Ƙwaƙwalwar Tsohon Shugaban Ƙasa Biden Yayin Mulkinsa

3 days ago
Tawagar MDD Da Majalisar Shugabancin Libya Sun Kafa Kwamitin Tsagaita Bude Wuta
Kasashen Ketare

Tawagar MDD Da Majalisar Shugabancin Libya Sun Kafa Kwamitin Tsagaita Bude Wuta

2 weeks ago
Trump Zai Shirya Liyafar Musamman Ga Manyan Ƴan Crypto 
Kasashen Ketare

Trump Zai Shirya Liyafar Musamman Ga Manyan Ƴan Crypto 

2 weeks ago
Abin Da Ya Sa Putin Ke Samun Karfin Iko Fiye Da Kowane Lokaci
Kasashen Ketare

Rasha Ta Ce Za Ta Tattauna Da Ukraine Don Yin Sulhu Game Da Yaƙin Da Suke Tafkawa

3 weeks ago
Sarkin Saudiyya Ya Ɗauki Nauyin Falasɗinawa 1,000 Su Sauke Farali
Kasashen Ketare

Sarkin Saudiyya Ya Ɗauki Nauyin Falasɗinawa 1,000 Su Sauke Farali

3 weeks ago
Birtaniya Ta Fitar Da Sabbin Tsauraran Dokokin Zama A Ƙasar
Kasashen Ketare

Birtaniya Ta Fitar Da Sabbin Tsauraran Dokokin Zama A Ƙasar

3 weeks ago
Next Post
Babu Wani Shiri Na Kwaso ‘Yan Nijeriya Daga Falasdin Ko Isra’ila –Gwamnatin Tarayya

Tinubu Ya Taya Sheikh Dahiru Bauchi Murnar Cika Shekaru 100

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.