• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masana Sun Bayyana Matsalolin Fina-finan Hausa Da Hanyoyin Inganta Su

by Rabilu Sanusi Bena
11 months ago
in Nishadi
0
Masana Sun Bayyana Matsalolin Fina-finan Hausa Da Hanyoyin Inganta Su
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jami’ar Usmanu Danfodiyo da ke Sakkwato ta daura damarar dawo wa da kima da martabar fina-finan Hausa a idon duniya ta hanyar daidaita yadda ake shirya su domin su dace da al’adar Malam Bahaushe da zamantakewar magidanta a kasar Hausa.

  • Hajji 2024: Sarki Salman Na Saudiyya Ya Bai Wa Mahajjata Kyautar Al-Æ™ur’ani Mai Girma
  • Kwamitin Tsakiyar Jami’iyyar Kwaminis Ta Kasar Sin Ya Kira Taron Ba Mambobinsa Ba

A kan wannan ne jami’ar ta shirya taron masana da kwararru kan tasiri, matsaloli da alkiblar da ya kamata fina-finan su dosa, wanda aka gudanar ta manhajar zoom a kafar sadarwar intanet.

  • Rikicin Sarautar Kano: Yadda Gwamnatin Abba Ta Sauya Alkibla
  • A Watan Mayu Za A Bude Bikin Baje Kolin Motoci Na Afrika A Legas
  • Amurka: Sarkin Leken Asiri Na Neman Habaka Karfinta

Masana da masu ruwa da tsaki a farfajiyar ilimi sun tattauna tare da fitar da tsaki da tsakuwa a taron da aka yi wa taken “Fina-fiinan Hausa da Zamantakewar Magidanta: Ina Aka Dosa?” a karkashin jagorancin Farfesa Abdallah Uba Adamu na tsangayar sadarwa da ke jami’ar Bayero, Kano.

Shehunan Malaman jami’a, fitattun malaman addini da masu ruwa da tsaki a sha’anin fina-finan Hausa da suka tattauna a taron na yini daya su ne, Aliyu Muhammad Bunza wanda shi ne Farfesan al’adun Hausawa na farko a duniya, wanda ya gabatar da mukala mai taken “Zamantakewar Auren Hausawa da Al’adun Hausawa.” Haka ma Farfesa Ibrahim Aliyu Malumfashi ya gabatar da takarda mai taken “Samuwar Fina-finai da Canjin Manufarsu da Aka Samu.”

Fitaccen maruubuci, jarumi kuma mai shirya fina-finan Hausa, Ado Ahmed Gidan Dabino wanda shi ne shugaban kungiyar masu shirya fina-finan Hausa ta Jihar Kano (MOPPAN) ya gabatar da mukala mai taken ‘Manufa da Gudunmuwar Fina-finan Hausa ga Zamantakewar Hausawa.”

Labarai Masu Nasaba

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

Ita kuwa Hadiza Salihu Koko daga kwalejin ilimi ta Shehu Shagari ta gabatar da kasida mai taken “Tasirin Fina-finan Hausa ga Zamantakewar Ma’aurata,” sai Sheikh Aminu Daurawa, shugaban Hukumar Hisbah Kano ya gabatar da takardar da ya rada wa sunan “Zamantakewar Ma’aurata a Addinin Musulunci Akasin yadda take a Fina-finan Hausa.”

Masanan sun cimma matsayar cewar fina-finan Hausa da aka fara shiryawa a

can baya an tsara su da gina su da haska su a akwatunan talabijin a bisa ga manufar fadakar da al’umma da ilmantar da su a kan shirye- shiryen ayyukan gwamnati akasin manufofin neman kudi na fina-finan wannan zamani.

“An lura da cewa al’umma suna taka muhimıniyar rawa wajen yaduwa da yawaitar kallon wadannan fina-finan Hausa da amfani da darussan da suke cikinsu masu alfanu da akasin haka.”

Tatttaunawa a taron an samu nasarar gano gurbatacciyar hanyar da masu shirya fina-finan suke ake yi wadda ke bukatar gyara domin kuwa sun cimma matsayar cewar, “fina-finan Hausa na wannan zamani sun saba wa al’adun Hausawa na asali baki daya na zamantakewa da kunya da sutura da tarbiyya, kuma suna haddasa matsalolin rashin fahimta da rabuwar aure atsakanin ma’aurata.”

Duka baya ga wannan kusoshin taron sun yi iyo da ninkaya tare da fito da shawarwari da hanyoyin da suke ganin su ne mafita wajen shirya fina-finan da Hausa da Hausawa za su yi alfahari da su a duniyar Malam Bahaushe, wadanda suka hada da: “shirya fina-finan Hausa wadanda suke

nuna darussan kyawawan al’adun zamantakewar auren Hausawa na tarbiyya da kunya da biyayya tsakanin ma’aurata da ‘ya’yansu kamar yadda wasannin kwaikwayo na da suka nuna.”

A cewarsu, “Bai kamata fina-finan Hausa na wannan zamani su mayar da hankali ga sana’ar neman kudi kawai ba, akasin fadakarwa da ilmantarwa da koyar da kyawawan al’adu da dabi’un Hausawa. Akwai bukatar magidanta da sauran al’ummar Hausawa su kauce wa kallon fina-finan Hausa na wannan zamani wadanda suka saba wa al’adu da addini da tarbiyyar Hausawa, wannan zai rage yaduwar fina-finan da amfani da miyagun darussan da ke cikinsu.”

Jagororin taron wadanda suka bayyana cewar za a ci gaba da gudanar da taron a nan gaba sun kuma ba da shawarar cewar, masana da manazarta su mayar da hankali sosai wajen rubutawa da shirya fina-finan Hausa masu koyar da kyawawan al’adu da dabi’un Hausawa, Gwamnati kuwa ta tallafa wajen daukar nauyin samar da su da yada su.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Adam ZangoAli NuhuFilmHausa FilmKannywood
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Sace Wayoyin Salula Sama Da Dubu 83 A Ingila A Cewar Rahotan ‘Yansandan Ƙasar

Next Post

HaÆ™ar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba: Nijeriya Na Asarar Naira Biliyan 9 Duk Shekara – Majalisa

Related

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu
Nishadi

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

6 days ago
Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 
Nishadi

Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

2 weeks ago
Hukuma Ta Dakatar Da Haska Fina-Finai 22 Har Sai Baba Tagani
Nishadi

Hukuma Ta Dakatar Da Haska Fina-Finai 22 Har Sai Baba Tagani

3 weeks ago
Ban ÆŠauki Harkar Fim Da Wasa Ba – Hauwa Ayawa
Nishadi

Ban ÆŠauki Harkar Fim Da Wasa Ba – Hauwa Ayawa

3 weeks ago
Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro
Nishadi

Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro

4 weeks ago
Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage
Nishadi

Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage

4 weeks ago
Next Post
HaÆ™ar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba: Nijeriya Na Asarar Naira Biliyan 9 Duk Shekara – Majalisa

Haƙar Ma'adinai Ba Bisa Ƙa'ida Ba: Nijeriya Na Asarar Naira Biliyan 9 Duk Shekara - Majalisa

LABARAI MASU NASABA

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

June 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

June 6, 2025
Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.