ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masana Sun Bayyana Matsalolin Fina-finan Hausa Da Hanyoyin Inganta Su

by Rabilu Sanusi Bena
2 years ago
Matsaloli

Jami’ar Usmanu Danfodiyo da ke Sakkwato ta daura damarar dawo wa da kima da martabar fina-finan Hausa a idon duniya ta hanyar daidaita yadda ake shirya su domin su dace da al’adar Malam Bahaushe da zamantakewar magidanta a kasar Hausa.

  • Hajji 2024: Sarki Salman Na Saudiyya Ya Bai Wa Mahajjata Kyautar Al-ƙur’ani Mai Girma
  • Kwamitin Tsakiyar Jami’iyyar Kwaminis Ta Kasar Sin Ya Kira Taron Ba Mambobinsa Ba

A kan wannan ne jami’ar ta shirya taron masana da kwararru kan tasiri, matsaloli da alkiblar da ya kamata fina-finan su dosa, wanda aka gudanar ta manhajar zoom a kafar sadarwar intanet.

  • Rikicin Sarautar Kano: Yadda Gwamnatin Abba Ta Sauya Alkibla
  • A Watan Mayu Za A Bude Bikin Baje Kolin Motoci Na Afrika A Legas
  • Amurka: Sarkin Leken Asiri Na Neman Habaka Karfinta

Masana da masu ruwa da tsaki a farfajiyar ilimi sun tattauna tare da fitar da tsaki da tsakuwa a taron da aka yi wa taken “Fina-fiinan Hausa da Zamantakewar Magidanta: Ina Aka Dosa?” a karkashin jagorancin Farfesa Abdallah Uba Adamu na tsangayar sadarwa da ke jami’ar Bayero, Kano.

ADVERTISEMENT

Shehunan Malaman jami’a, fitattun malaman addini da masu ruwa da tsaki a sha’anin fina-finan Hausa da suka tattauna a taron na yini daya su ne, Aliyu Muhammad Bunza wanda shi ne Farfesan al’adun Hausawa na farko a duniya, wanda ya gabatar da mukala mai taken “Zamantakewar Auren Hausawa da Al’adun Hausawa.” Haka ma Farfesa Ibrahim Aliyu Malumfashi ya gabatar da takarda mai taken “Samuwar Fina-finai da Canjin Manufarsu da Aka Samu.”

Fitaccen maruubuci, jarumi kuma mai shirya fina-finan Hausa, Ado Ahmed Gidan Dabino wanda shi ne shugaban kungiyar masu shirya fina-finan Hausa ta Jihar Kano (MOPPAN) ya gabatar da mukala mai taken ‘Manufa da Gudunmuwar Fina-finan Hausa ga Zamantakewar Hausawa.”

LABARAI MASU NASABA

Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

Ita kuwa Hadiza Salihu Koko daga kwalejin ilimi ta Shehu Shagari ta gabatar da kasida mai taken “Tasirin Fina-finan Hausa ga Zamantakewar Ma’aurata,” sai Sheikh Aminu Daurawa, shugaban Hukumar Hisbah Kano ya gabatar da takardar da ya rada wa sunan “Zamantakewar Ma’aurata a Addinin Musulunci Akasin yadda take a Fina-finan Hausa.”

Masanan sun cimma matsayar cewar fina-finan Hausa da aka fara shiryawa a

can baya an tsara su da gina su da haska su a akwatunan talabijin a bisa ga manufar fadakar da al’umma da ilmantar da su a kan shirye- shiryen ayyukan gwamnati akasin manufofin neman kudi na fina-finan wannan zamani.

“An lura da cewa al’umma suna taka muhimıniyar rawa wajen yaduwa da yawaitar kallon wadannan fina-finan Hausa da amfani da darussan da suke cikinsu masu alfanu da akasin haka.”

Tatttaunawa a taron an samu nasarar gano gurbatacciyar hanyar da masu shirya fina-finan suke ake yi wadda ke bukatar gyara domin kuwa sun cimma matsayar cewar, “fina-finan Hausa na wannan zamani sun saba wa al’adun Hausawa na asali baki daya na zamantakewa da kunya da sutura da tarbiyya, kuma suna haddasa matsalolin rashin fahimta da rabuwar aure atsakanin ma’aurata.”

Duka baya ga wannan kusoshin taron sun yi iyo da ninkaya tare da fito da shawarwari da hanyoyin da suke ganin su ne mafita wajen shirya fina-finan da Hausa da Hausawa za su yi alfahari da su a duniyar Malam Bahaushe, wadanda suka hada da: “shirya fina-finan Hausa wadanda suke

nuna darussan kyawawan al’adun zamantakewar auren Hausawa na tarbiyya da kunya da biyayya tsakanin ma’aurata da ‘ya’yansu kamar yadda wasannin kwaikwayo na da suka nuna.”

A cewarsu, “Bai kamata fina-finan Hausa na wannan zamani su mayar da hankali ga sana’ar neman kudi kawai ba, akasin fadakarwa da ilmantarwa da koyar da kyawawan al’adu da dabi’un Hausawa. Akwai bukatar magidanta da sauran al’ummar Hausawa su kauce wa kallon fina-finan Hausa na wannan zamani wadanda suka saba wa al’adu da addini da tarbiyyar Hausawa, wannan zai rage yaduwar fina-finan da amfani da miyagun darussan da ke cikinsu.”

Jagororin taron wadanda suka bayyana cewar za a ci gaba da gudanar da taron a nan gaba sun kuma ba da shawarar cewar, masana da manazarta su mayar da hankali sosai wajen rubutawa da shirya fina-finan Hausa masu koyar da kyawawan al’adu da dabi’un Hausawa, Gwamnati kuwa ta tallafa wajen daukar nauyin samar da su da yada su.”

Matsaloli
Rabilu Sanusi Bena
+ postsBio
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Turkiyya Ta Zama Ƙasa Ta Biyu Da Ta Fice Daga Gasar Kofin Duniya
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

MASU ALAKA

Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina
Nishadi

Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina

June 14, 2026
Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi
Nishadi

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

June 14, 2026
Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro
Nishadi

Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro

May 31, 2026
Next Post
Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba: Nijeriya Na Asarar Naira Biliyan 9 Duk Shekara – Majalisa

Haƙar Ma'adinai Ba Bisa Ƙa'ida Ba: Nijeriya Na Asarar Naira Biliyan 9 Duk Shekara - Majalisa

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.