ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masana Sun Bayyana Matsalolin Fina-finan Hausa Da Hanyoyin Inganta Su

by Rabilu Sanusi Bena
2 years ago
Matsaloli

Jami’ar Usmanu Danfodiyo da ke Sakkwato ta daura damarar dawo wa da kima da martabar fina-finan Hausa a idon duniya ta hanyar daidaita yadda ake shirya su domin su dace da al’adar Malam Bahaushe da zamantakewar magidanta a kasar Hausa.

  • Hajji 2024: Sarki Salman Na Saudiyya Ya Bai Wa Mahajjata Kyautar Al-ƙur’ani Mai Girma
  • Kwamitin Tsakiyar Jami’iyyar Kwaminis Ta Kasar Sin Ya Kira Taron Ba Mambobinsa Ba

A kan wannan ne jami’ar ta shirya taron masana da kwararru kan tasiri, matsaloli da alkiblar da ya kamata fina-finan su dosa, wanda aka gudanar ta manhajar zoom a kafar sadarwar intanet.

  • Rikicin Sarautar Kano: Yadda Gwamnatin Abba Ta Sauya Alkibla
  • A Watan Mayu Za A Bude Bikin Baje Kolin Motoci Na Afrika A Legas
  • Amurka: Sarkin Leken Asiri Na Neman Habaka Karfinta

Masana da masu ruwa da tsaki a farfajiyar ilimi sun tattauna tare da fitar da tsaki da tsakuwa a taron da aka yi wa taken “Fina-fiinan Hausa da Zamantakewar Magidanta: Ina Aka Dosa?” a karkashin jagorancin Farfesa Abdallah Uba Adamu na tsangayar sadarwa da ke jami’ar Bayero, Kano.

ADVERTISEMENT

Shehunan Malaman jami’a, fitattun malaman addini da masu ruwa da tsaki a sha’anin fina-finan Hausa da suka tattauna a taron na yini daya su ne, Aliyu Muhammad Bunza wanda shi ne Farfesan al’adun Hausawa na farko a duniya, wanda ya gabatar da mukala mai taken “Zamantakewar Auren Hausawa da Al’adun Hausawa.” Haka ma Farfesa Ibrahim Aliyu Malumfashi ya gabatar da takarda mai taken “Samuwar Fina-finai da Canjin Manufarsu da Aka Samu.”

Fitaccen maruubuci, jarumi kuma mai shirya fina-finan Hausa, Ado Ahmed Gidan Dabino wanda shi ne shugaban kungiyar masu shirya fina-finan Hausa ta Jihar Kano (MOPPAN) ya gabatar da mukala mai taken ‘Manufa da Gudunmuwar Fina-finan Hausa ga Zamantakewar Hausawa.”

LABARAI MASU NASABA

Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa

Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

Ita kuwa Hadiza Salihu Koko daga kwalejin ilimi ta Shehu Shagari ta gabatar da kasida mai taken “Tasirin Fina-finan Hausa ga Zamantakewar Ma’aurata,” sai Sheikh Aminu Daurawa, shugaban Hukumar Hisbah Kano ya gabatar da takardar da ya rada wa sunan “Zamantakewar Ma’aurata a Addinin Musulunci Akasin yadda take a Fina-finan Hausa.”

Masanan sun cimma matsayar cewar fina-finan Hausa da aka fara shiryawa a

can baya an tsara su da gina su da haska su a akwatunan talabijin a bisa ga manufar fadakar da al’umma da ilmantar da su a kan shirye- shiryen ayyukan gwamnati akasin manufofin neman kudi na fina-finan wannan zamani.

“An lura da cewa al’umma suna taka muhimıniyar rawa wajen yaduwa da yawaitar kallon wadannan fina-finan Hausa da amfani da darussan da suke cikinsu masu alfanu da akasin haka.”

Tatttaunawa a taron an samu nasarar gano gurbatacciyar hanyar da masu shirya fina-finan suke ake yi wadda ke bukatar gyara domin kuwa sun cimma matsayar cewar, “fina-finan Hausa na wannan zamani sun saba wa al’adun Hausawa na asali baki daya na zamantakewa da kunya da sutura da tarbiyya, kuma suna haddasa matsalolin rashin fahimta da rabuwar aure atsakanin ma’aurata.”

Duka baya ga wannan kusoshin taron sun yi iyo da ninkaya tare da fito da shawarwari da hanyoyin da suke ganin su ne mafita wajen shirya fina-finan da Hausa da Hausawa za su yi alfahari da su a duniyar Malam Bahaushe, wadanda suka hada da: “shirya fina-finan Hausa wadanda suke

nuna darussan kyawawan al’adun zamantakewar auren Hausawa na tarbiyya da kunya da biyayya tsakanin ma’aurata da ‘ya’yansu kamar yadda wasannin kwaikwayo na da suka nuna.”

A cewarsu, “Bai kamata fina-finan Hausa na wannan zamani su mayar da hankali ga sana’ar neman kudi kawai ba, akasin fadakarwa da ilmantarwa da koyar da kyawawan al’adu da dabi’un Hausawa. Akwai bukatar magidanta da sauran al’ummar Hausawa su kauce wa kallon fina-finan Hausa na wannan zamani wadanda suka saba wa al’adu da addini da tarbiyyar Hausawa, wannan zai rage yaduwar fina-finan da amfani da miyagun darussan da ke cikinsu.”

Jagororin taron wadanda suka bayyana cewar za a ci gaba da gudanar da taron a nan gaba sun kuma ba da shawarar cewar, masana da manazarta su mayar da hankali sosai wajen rubutawa da shirya fina-finan Hausa masu koyar da kyawawan al’adu da dabi’un Hausawa, Gwamnati kuwa ta tallafa wajen daukar nauyin samar da su da yada su.”

Matsaloli
Rabilu Sanusi Bena
+ postsBio
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Za’a Dakatar Da Wasa A Farkon Minti 10 Na Kowane Wasa A Kasar Argentina Saboda Girmama Messi
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Chelsea Ta Kammala Ɗaukar Ahanor Kan Fam Miliyan 40

MASU ALAKA

Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
Nishadi

Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa

September 5, 2026
Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood
Nishadi

Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

August 29, 2026
Matsaloli
Nishadi

Dalilan Da Suka Sa Ba Zan Iya Auren Ɗan Film Ba —Bilkisu Bishasha

August 23, 2026
Next Post
Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba: Nijeriya Na Asarar Naira Biliyan 9 Duk Shekara – Majalisa

Haƙar Ma'adinai Ba Bisa Ƙa'ida Ba: Nijeriya Na Asarar Naira Biliyan 9 Duk Shekara - Majalisa

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.