ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba: Nijeriya Na Asarar Naira Biliyan 9 Duk Shekara – Majalisa

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Nijeriya

Kwamitin majalisar wakilai kan albartun kasa, ya ce Nijeriya tana tafka asarar naira biliyan 9 a kowace shekara sakamakon aikace-aikacen masu hakar ma’adinai ta haramtattun hanyoyi a Nijeriya.

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da rundunar sojin Nijeriya ta ce, ta cafke wadanda take zargi da hannu a hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba su 387 a cikin watanni bakwai da suka gabata.

  • Ramin Haƙar Ma’adanai Ya Rufta Da Mutum 3 A Jihar Neja
  • Miyar Agushi Mai Dadi Irin Ta Yammacin Nijeriya

Shugaban kwamitin majalisar, Jonathan Gaza Gbefwi, shi ne ya shaida hakan a yayin taron jin bahasin jama’a da kwamitin ya shirya kan binciken lamuran da suka shafi hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba da na albartun kasa. Ya ce, wannan mummunar ayyukan satar ma’adinai ya janyo takaituwar jin gajiyar albartun da jama’an kasa ba su yi yadda ya dace.

ADVERTISEMENT

Ya koka kan cewa zallar kaso uku kawai cikin kamfanonin da ke hakar ma’adinai ne suka biya na kudin lasisi hakar ma’adinai a kasar nan.

A cewarsa, daga cikin illar da hako ma’adinai ta barauniyar hanya ke janyowa har da janyo matsalolin tsaro da kuma arangama kan wake ko su waye masu ikon jan ragamar wuraren hako ma’adinai da albartun da ke ciki.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Ya ce, irin wannan rigimar na fantsama har ya shafi siyasa da zamantakewar jama’an da ke yankunan da abun ya shafa, wanda hakan ba daidai ba ne sam.

Sannan ya kara da cewa taron jin bahasin an shirya ne da zimmar shawo kan matsalolin da suke tattare da aikace-aikacen hako ma’adinai da kuma inganta hanyoyin samar da lasisi domin kyautata samar wa kasar nan da kudaden shiga da kuma cin gajiyar ma’adinan da suke jibge a kasar ba tare da wasu matsaloli ba.

“Nijeriya tana rasa naira biliyan 9 a kowace shekara kan ayyukan masu hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba. Don haka, jagorancin majalisar wakilai ta 10 ya ga dacewar ya ji bahasin jama’a domin kawo gyara da mafita cikin wannan lamarin ta yadda za a samu gaskiya da adalci kan kudaden da suke shigowa domin inganta tattalin arzikin kasa.

“Ta’asar masu hako ma’adinai ba bisa ka’ida na gurgunta ci gaban da ake samu a bangaren ma’adinai, kuma yana janyo lalata muhalli da gurbacewarsa wanda ke janyo asarar kudaden shiga masu tulin yawa da ya dace jama’an da ke yankunan da abun ya shafa da ma kasa su mora.”

A fadin Jonathan, akwai bukatar a gaggauta daukan matakan da suak dace wajen dakile aniyar masu satar ma’adinai domin kyautata kudin shiga, kare jama’a da kuma tabbatar da duk masu hakar ma’adinai na bin dokokin kasa.

Shi kuma, shugaban sojojin Nijeriya, Janaral Christopher Musa, ya ce masu hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba suna samun goyon baya daga wasu fitattun mutane da suke ba su kariya.

Da yake bude taron jin bahasin jama’an, kakakin majalisar wakilai, Tajudeen Abbas, wanda ya samu wakilcin Farfesa Julius Ihonbbere, ya lura kan cewa satar ma’adinai na ruguza tattalin arzikin kasar nan, lamarin da a cewarsa yake kara jefa jama’a cikin fatara da talauci, musamman manoman da suka dogara da noma amma aka lalata musu muhallin da suke zama da sunan hakar ma’adinai.

Nijeriya
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Dattawan Yarabawa Da Ibo Sun Goyi Bayan Kafa Ma’aikatar Kiwo

Dattawan Yarabawa Da Ibo Sun Goyi Bayan Kafa Ma'aikatar Kiwo

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.