• English
  • Business News
Saturday, September 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Harbi Mutane 8, 4 Sun Mutu A Zanga-Zanga A Kano

by Sadiq
1 year ago
in Labarai
0
An Harbi Mutane 8, 4 Sun Mutu A Zanga-Zanga A Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ana fargabar mutane da dama sun mutu, yayin da wasu da dama kuma suka jikkata, sakamakon wani rikici da ya barke tsakanin ‘yan daba da jami’an tsaro a Jihar Kano.

Yankunan da lamarin ya shafa sun hada da Rijiyar Lemo, Kurna zuwa Bachirawa a karamar hukumar Fagge, Kofar Nassarawa a karamar hukumar Birni, da Unguwa Uku a karamar hukumar Tarauni.

  • Tinubu Zai Yi Wa ‘Yan Nijeriya Jawabi A Ranar Lahadi
  • Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

A cewar wasu shaidun gani da ido, arangamar ta fara ne a lokacin da wasu matasa suka bijirewa dokar hana fita da aka sanya a jihar tare da fitowa kan tituna, inda suka ci gaba da zanga-zangar da ta rikide zuwa tashin hankali a Kano.

Wani mazaunin Rijiyar Lemo mai suna Abdulkadir Musa ya ce, “Akalla mutane takwas ne aka harbe a yankinmu da suka hada da mata da yara. Yanzu haka wata tsohuwa ta mutu tare da wasu uku, yayin da da dama suka samu munanan raunuka.

“A gaskiya abin da ya faru shi ne, kun san har yanzu dokar hana fita tana nan, don haka mutane suka bijirewa hakan suka fito suna zanga-zanga. A lokacin ne jami’an tsaro suka fara kai farmaki, suna kokarin tarwatsa su, kuma ana cikin haka ne sai da suka yi harbin domin su tarwatsa masu zanga-zangar.”

Labarai Masu Nasaba

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Wani mazaunin garin, wanda ya bukaci a sakaya sunansa, ya ce ‘yan daban da suka fake da zanga-zangar yunwar, sun yi yunkurin fasa shaguna, ciki har da shagon Rufaida Yoghourt.

Ya ce jami’an tsaro sun tarwatsa ’yan daban, inda daga nan ne suka fara jifan su da duwatsu.

An bayyana cewa wani jami’in ‘yan sanda ya ji rauni a yayin arangamar, ko da yake ba a tantance shi ba har zuwa lokacin hada wannan rahoto.

Mutanen da harsashi ya rutsa da su yanzu haka suna samun kulawar likitoci a asibitin Salamatu.

Wata mai amfani da shafukan sada zumunta, Aiha K Nass, ta wallafa, “Muna nan muna makokin kakarmu; ‘yan sanda sun harbe yayana Aliyu. Yanzu haka ya mutu.”

Wani mai amfani da shafukan sada zumunta, Omar Khalid Saleh, ya rubuta cewa, “’Yan sanda a Kano sun mayar da zanga-zangar lumana zuwa wani abu daban. Me ya sa ake harbe-harbe da kashe-kashe? Kuna gayyatar matsala. Sun harbe wannan matashi ne, kuma ya mutu nan take a Kofar Nasarawa, cikin birnin Kano. #EndBadGovernance A Nijeriya #KarshenYanSanda.”

Masu zanga-zangar sun fito kan titin Zariya da ke kan Unguwa Uku amma kuma jami’an tsaro sun tarwatsa su.

An jibge karin jami’an tsaro domin dakile zirga-zirga a Kurna Asabe, kusa da Barikin Sojoji na Bukavu.

Kokarin jin ta bakin kakakin ‘yansandan jihar, ya ci tura domin har zuwa lokacin hada wannan rahoto, SP Abudullahi Haruna Kiyawa bai daga waya ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: HarbikanoKisaMutuwaRauniTarzomaZanga-zanga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Zai Yi Wa ‘Yan Nijeriya Jawabi A Ranar Lahadi

Next Post

An Yi Shawarwari Tsakanin Matasan Kasa Da Kasa A Wajen Taron Tattaunawa Mai Taken “Zurfafa Gyare-Gyare A Sin Dama Ce Ga Duniya”

Related

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta
Labarai

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

8 hours ago
Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?
Manyan Labarai

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

11 hours ago
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna
Manyan Labarai

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

11 hours ago
Kano
Labarai

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

13 hours ago
An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki
Labarai

An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki

14 hours ago
Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi
Labarai

Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

15 hours ago
Next Post
An Yi Shawarwari Tsakanin Matasan Kasa Da Kasa A Wajen Taron Tattaunawa Mai Taken “Zurfafa Gyare-Gyare A Sin Dama Ce Ga Duniya”

An Yi Shawarwari Tsakanin Matasan Kasa Da Kasa A Wajen Taron Tattaunawa Mai Taken “Zurfafa Gyare-Gyare A Sin Dama Ce Ga Duniya”

LABARAI MASU NASABA

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

September 19, 2025
Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

September 19, 2025
An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

September 19, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

September 19, 2025
Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

September 19, 2025
Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

September 19, 2025
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

September 19, 2025
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

September 19, 2025
Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

September 19, 2025
Kano

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

September 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.