• English
  • Business News
Thursday, August 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsalar Kifewar Kwale-kwale A Jihar Jigawa

by Leadership Hausa and Sulaiman
12 months ago
in Ra'ayoyi
0
Kifewar kwale-kwale
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Assalamu Alaikum, Editan Jaridar LEADERSHIP Hausa mai Albarka, da fatan alkairi ga dukkanin ma’aikatanku.

 

Hakika ya kamata gwamnatin jiharmu ta Jigawa ta dauki matakin gaggawa domin magance matsalar yawan samun kifewar kwale-kwale a sassan jihar duba da yadda wannan matsala take afkuwa a kai a kai a sassan wannan jiha tamu wanda hakan ke jawo asarar rayukan al’umma da dama, domin ya faru a garin Kalgwai ta Karamar Hukumar Auyo da garin Nahuche na Karamar Hukumar Taura da ma wani gari a Karamar Hukumar Buji duk a cikin dan karamin lokaci.

  • Fina-finai Masu Dogon Zango Koma Baya Ne Ga Masana’antar Kannywood – Tanimu Akawu
  • Amfani Da Kayan Marmarin Da Aka Jima Da Yankawa Na Haifar Da Matsala – Likita

Wannan matsala tana faruwa ce ta dalilin yin amfani da kwale-kwale marasa inganci, rashin yin amfani da rigar taimakon linkaya ma’ana (life jacket) da kuma zarin lodi da ake yi wa wadanan kwale-kwale, don haka ya kamata gwamnati ta dauki matakin magance wannan matsala.

 

Labarai Masu Nasaba

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri

Domin idan har gwamnati ta dauki matakin samar da gadoji, kananan kwale-kwale masu inji masu inganci da ma rigar taimakon linkaya ma’ana (life jacket) a wadanan gurare, hakika za a samu saukin wannan matsala, domin yawanci wadanan tafiye-tafiye da al’ummar wadanan yankuna suke yi a cikin kwale-kwalen suna yi domin zuwa gonakansu ko kuma kasuwanni wanda dukka dole ne sai an yi su domin hanyoyi ne na gudanar da rayuwar yau da kullum ta al’umma.

 

Akwai fa yankuna da dama da ke fama da irin wannan matsala ko a Karamar Hukumar Miga akwai mahayin kogi da ke yankin mazabar Sansani da ke fama da irin wannan matsala a duk lokacin damina.

 

Tabbas wannan matsala ta kifewar kwale-kwale matsala ce da ta jima tana faruwa a sassan kananan hukumomi na jiharmu ta Jigawa, duba da yadda wannan matsala take faruwa duk shekara ya kamata gwamnati ta yi dukkanin abin da ya dace domin magance matsalar, tunda babban aikin gwamnati shi ne kare rayukan al’umma da dukiyarsu.

 

Hakika wadanan yankuna da ake fuskantar wannan matsala ta kifewar kwale-kwale suna da matukar tasiri da muhimmanci a tattalin arzikin jiharmu domin yankuna ne da ake noman rani da damina ga kuma sana’ar kamun kifi ko su da kuma kiwon dabobi, don haka sun cancanci a ba su kulawa domin kare rayukan al’umma da dama habaka tattalin arzikin jiharmu.

 

Tabbas ya kamata gwamnati ta yi kokarin hada hannu da jami’an tsaro wajen kula da irin wadanan yankuna da ake tafiye-tafiye a cikin ruwa, domin rage lodin jama’a da kaya da ake yi wa wadanan kwale-kwale da ya yi yawa.

 

Daga karshe nake addu’ar Allah ya yi riko da hannayen Gwamna Malam Umar Namadi Danmodi wajen magance wannan matsala dama gudanar da mulkin jiharmu ta Jigawa don alfarmar Annabin Rahama (S.A.W).

[email protected].


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Mai Martaba Sarkin Ningi Ya Rasu Yana Da Shekara 88

Next Post

DSS Ta Kama Tsohon Editan BBC, Adejuwon Soyinka A Filin Jirgin Sama Na Legas

Related

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 
Ra'ayoyi

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

5 months ago
Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri
Ra'ayoyi

Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri

9 months ago
Nijeriya
Ra'ayoyi

Ra’ayoyin ‘Yan Nijeriya A Kan Zagayowar Ranar Samun ‘Yancin Kai

10 months ago
Shekara 64 Da Samun ‘Yanci: Maimakon Biki, Jajantawa Ya Kamata A Yi – ‘Yan Nijeriya
Ra'ayoyi

Shekara 64 Da Samun ‘Yanci: Maimakon Biki, Jajantawa Ya Kamata A Yi – ‘Yan Nijeriya

10 months ago
Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano
Ra'ayoyi

Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano

10 months ago
Dauda Lawal A Shekara 59: Mai Gidana Wanda Bai Da Jiji Da Kai
Ra'ayoyi

Dauda Lawal A Shekara 59: Mai Gidana Wanda Bai Da Jiji Da Kai

11 months ago
Next Post
DSS Ta Kama Tsohon Editan BBC, Adejuwon Soyinka A Filin Jirgin Sama Na Legas

DSS Ta Kama Tsohon Editan BBC, Adejuwon Soyinka A Filin Jirgin Sama Na Legas

LABARAI MASU NASABA

Jami’an Tsaro Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara, Sun Ƙwato Bindigogi

Jami’an Tsaro Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara, Sun Ƙwato Bindigogi

August 7, 2025
An Bude Bikin Fina-Finan Kasar Sin A Zimbabwe

An Bude Bikin Fina-Finan Kasar Sin A Zimbabwe

August 7, 2025
Jama’a Suke Tona Asirin Gurɓatattun Jami’anmu – Kwamishinan ‘Yansandan Kano

Jama’a Suke Tona Asirin Gurɓatattun Jami’anmu – Kwamishinan ‘Yansandan Kano

August 7, 2025
Yawancin ‘Yan Siyasar Nijeriya Ba Su Da Tarbiyya – Sarki Sanusi II

Yawancin ‘Yan Siyasar Nijeriya Ba Su Da Tarbiyya – Sarki Sanusi II

August 7, 2025
Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

August 6, 2025
Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

August 6, 2025
Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

August 6, 2025
Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

August 6, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Bayar Da Kiwon Lafiya Kyauta Ga ‘Yan Fansho Masu Karamin Karfi 

August 6, 2025
Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping

Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping

August 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.