• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsalar Kifewar Kwale-kwale A Jihar Jigawa

byLeadership Hausa and Sulaiman
1 year ago
Kifewar kwale-kwale

Assalamu Alaikum, Editan Jaridar LEADERSHIP Hausa mai Albarka, da fatan alkairi ga dukkanin ma’aikatanku.

 

Hakika ya kamata gwamnatin jiharmu ta Jigawa ta dauki matakin gaggawa domin magance matsalar yawan samun kifewar kwale-kwale a sassan jihar duba da yadda wannan matsala take afkuwa a kai a kai a sassan wannan jiha tamu wanda hakan ke jawo asarar rayukan al’umma da dama, domin ya faru a garin Kalgwai ta Karamar Hukumar Auyo da garin Nahuche na Karamar Hukumar Taura da ma wani gari a Karamar Hukumar Buji duk a cikin dan karamin lokaci.

  • Fina-finai Masu Dogon Zango Koma Baya Ne Ga Masana’antar Kannywood – Tanimu Akawu
  • Amfani Da Kayan Marmarin Da Aka Jima Da Yankawa Na Haifar Da Matsala – Likita

Wannan matsala tana faruwa ce ta dalilin yin amfani da kwale-kwale marasa inganci, rashin yin amfani da rigar taimakon linkaya ma’ana (life jacket) da kuma zarin lodi da ake yi wa wadanan kwale-kwale, don haka ya kamata gwamnati ta dauki matakin magance wannan matsala.

 

LABARAI MASU NASABA

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri

Domin idan har gwamnati ta dauki matakin samar da gadoji, kananan kwale-kwale masu inji masu inganci da ma rigar taimakon linkaya ma’ana (life jacket) a wadanan gurare, hakika za a samu saukin wannan matsala, domin yawanci wadanan tafiye-tafiye da al’ummar wadanan yankuna suke yi a cikin kwale-kwalen suna yi domin zuwa gonakansu ko kuma kasuwanni wanda dukka dole ne sai an yi su domin hanyoyi ne na gudanar da rayuwar yau da kullum ta al’umma.

 

Akwai fa yankuna da dama da ke fama da irin wannan matsala ko a Karamar Hukumar Miga akwai mahayin kogi da ke yankin mazabar Sansani da ke fama da irin wannan matsala a duk lokacin damina.

 

Tabbas wannan matsala ta kifewar kwale-kwale matsala ce da ta jima tana faruwa a sassan kananan hukumomi na jiharmu ta Jigawa, duba da yadda wannan matsala take faruwa duk shekara ya kamata gwamnati ta yi dukkanin abin da ya dace domin magance matsalar, tunda babban aikin gwamnati shi ne kare rayukan al’umma da dukiyarsu.

 

Hakika wadanan yankuna da ake fuskantar wannan matsala ta kifewar kwale-kwale suna da matukar tasiri da muhimmanci a tattalin arzikin jiharmu domin yankuna ne da ake noman rani da damina ga kuma sana’ar kamun kifi ko su da kuma kiwon dabobi, don haka sun cancanci a ba su kulawa domin kare rayukan al’umma da dama habaka tattalin arzikin jiharmu.

 

Tabbas ya kamata gwamnati ta yi kokarin hada hannu da jami’an tsaro wajen kula da irin wadanan yankuna da ake tafiye-tafiye a cikin ruwa, domin rage lodin jama’a da kaya da ake yi wa wadanan kwale-kwale da ya yi yawa.

 

Daga karshe nake addu’ar Allah ya yi riko da hannayen Gwamna Malam Umar Namadi Danmodi wajen magance wannan matsala dama gudanar da mulkin jiharmu ta Jigawa don alfarmar Annabin Rahama (S.A.W).

[email protected].

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 
Ra'ayoyi

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

March 18, 2025
Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri
Ra'ayoyi

Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri

November 10, 2024
Nijeriya
Ra'ayoyi

Ra’ayoyin ‘Yan Nijeriya A Kan Zagayowar Ranar Samun ‘Yancin Kai

October 5, 2024
Next Post
DSS Ta Kama Tsohon Editan BBC, Adejuwon Soyinka A Filin Jirgin Sama Na Legas

DSS Ta Kama Tsohon Editan BBC, Adejuwon Soyinka A Filin Jirgin Sama Na Legas

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version