ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsalar Kifewar Kwale-kwale A Jihar Jigawa

by Leadership Hausa and Sulaiman
2 years ago
Kifewar kwale-kwale

Assalamu Alaikum, Editan Jaridar LEADERSHIP Hausa mai Albarka, da fatan alkairi ga dukkanin ma’aikatanku.

 

Hakika ya kamata gwamnatin jiharmu ta Jigawa ta dauki matakin gaggawa domin magance matsalar yawan samun kifewar kwale-kwale a sassan jihar duba da yadda wannan matsala take afkuwa a kai a kai a sassan wannan jiha tamu wanda hakan ke jawo asarar rayukan al’umma da dama, domin ya faru a garin Kalgwai ta Karamar Hukumar Auyo da garin Nahuche na Karamar Hukumar Taura da ma wani gari a Karamar Hukumar Buji duk a cikin dan karamin lokaci.

ADVERTISEMENT
  • Fina-finai Masu Dogon Zango Koma Baya Ne Ga Masana’antar Kannywood – Tanimu Akawu
  • Amfani Da Kayan Marmarin Da Aka Jima Da Yankawa Na Haifar Da Matsala – Likita

Wannan matsala tana faruwa ce ta dalilin yin amfani da kwale-kwale marasa inganci, rashin yin amfani da rigar taimakon linkaya ma’ana (life jacket) da kuma zarin lodi da ake yi wa wadanan kwale-kwale, don haka ya kamata gwamnati ta dauki matakin magance wannan matsala.

 

LABARAI MASU NASABA

Gwarzo Na Shirin Sake Fitowa Domin Kawo Sabbin Salon Siyasa A Kano

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

Domin idan har gwamnati ta dauki matakin samar da gadoji, kananan kwale-kwale masu inji masu inganci da ma rigar taimakon linkaya ma’ana (life jacket) a wadanan gurare, hakika za a samu saukin wannan matsala, domin yawanci wadanan tafiye-tafiye da al’ummar wadanan yankuna suke yi a cikin kwale-kwalen suna yi domin zuwa gonakansu ko kuma kasuwanni wanda dukka dole ne sai an yi su domin hanyoyi ne na gudanar da rayuwar yau da kullum ta al’umma.

 

Akwai fa yankuna da dama da ke fama da irin wannan matsala ko a Karamar Hukumar Miga akwai mahayin kogi da ke yankin mazabar Sansani da ke fama da irin wannan matsala a duk lokacin damina.

 

Tabbas wannan matsala ta kifewar kwale-kwale matsala ce da ta jima tana faruwa a sassan kananan hukumomi na jiharmu ta Jigawa, duba da yadda wannan matsala take faruwa duk shekara ya kamata gwamnati ta yi dukkanin abin da ya dace domin magance matsalar, tunda babban aikin gwamnati shi ne kare rayukan al’umma da dukiyarsu.

 

Hakika wadanan yankuna da ake fuskantar wannan matsala ta kifewar kwale-kwale suna da matukar tasiri da muhimmanci a tattalin arzikin jiharmu domin yankuna ne da ake noman rani da damina ga kuma sana’ar kamun kifi ko su da kuma kiwon dabobi, don haka sun cancanci a ba su kulawa domin kare rayukan al’umma da dama habaka tattalin arzikin jiharmu.

 

Tabbas ya kamata gwamnati ta yi kokarin hada hannu da jami’an tsaro wajen kula da irin wadanan yankuna da ake tafiye-tafiye a cikin ruwa, domin rage lodin jama’a da kaya da ake yi wa wadanan kwale-kwale da ya yi yawa.

 

Daga karshe nake addu’ar Allah ya yi riko da hannayen Gwamna Malam Umar Namadi Danmodi wajen magance wannan matsala dama gudanar da mulkin jiharmu ta Jigawa don alfarmar Annabin Rahama (S.A.W).

[email protected].

Kifewar kwale-kwale
Leadership Hausa
Website |  + posts Bio
  • Leadership Hausa
    Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja
  • Leadership Hausa
    Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed
  • Leadership Hausa
    Batun Dawo Da Tallafin Mai Da Atiku Ya Yi Na Ci Gaba Da Tayar Da Kura
  • Leadership Hausa
    Batun Guguwar Kakar Yakin Neman Zabukan 2027 A Nijeriya
Kifewar kwale-kwale
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

Gwarzo Na Shirin Sake Fitowa Domin Kawo Sabbin Salon Siyasa A Kano
Siyasa

Gwarzo Na Shirin Sake Fitowa Domin Kawo Sabbin Salon Siyasa A Kano

April 25, 2026
Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 
Ra'ayoyi

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

March 18, 2025
Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri
Ra'ayoyi

Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri

November 10, 2024
Next Post
DSS Ta Kama Tsohon Editan BBC, Adejuwon Soyinka A Filin Jirgin Sama Na Legas

DSS Ta Kama Tsohon Editan BBC, Adejuwon Soyinka A Filin Jirgin Sama Na Legas

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.