ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsalar Kifewar Kwale-kwale A Jihar Jigawa

by Leadership Hausa and Sulaiman
2 years ago
Kifewar kwale-kwale

Assalamu Alaikum, Editan Jaridar LEADERSHIP Hausa mai Albarka, da fatan alkairi ga dukkanin ma’aikatanku.

 

Hakika ya kamata gwamnatin jiharmu ta Jigawa ta dauki matakin gaggawa domin magance matsalar yawan samun kifewar kwale-kwale a sassan jihar duba da yadda wannan matsala take afkuwa a kai a kai a sassan wannan jiha tamu wanda hakan ke jawo asarar rayukan al’umma da dama, domin ya faru a garin Kalgwai ta Karamar Hukumar Auyo da garin Nahuche na Karamar Hukumar Taura da ma wani gari a Karamar Hukumar Buji duk a cikin dan karamin lokaci.

ADVERTISEMENT
  • Fina-finai Masu Dogon Zango Koma Baya Ne Ga Masana’antar Kannywood – Tanimu Akawu
  • Amfani Da Kayan Marmarin Da Aka Jima Da Yankawa Na Haifar Da Matsala – Likita

Wannan matsala tana faruwa ce ta dalilin yin amfani da kwale-kwale marasa inganci, rashin yin amfani da rigar taimakon linkaya ma’ana (life jacket) da kuma zarin lodi da ake yi wa wadanan kwale-kwale, don haka ya kamata gwamnati ta dauki matakin magance wannan matsala.

 

LABARAI MASU NASABA

Gwarzo Na Shirin Sake Fitowa Domin Kawo Sabbin Salon Siyasa A Kano

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

Domin idan har gwamnati ta dauki matakin samar da gadoji, kananan kwale-kwale masu inji masu inganci da ma rigar taimakon linkaya ma’ana (life jacket) a wadanan gurare, hakika za a samu saukin wannan matsala, domin yawanci wadanan tafiye-tafiye da al’ummar wadanan yankuna suke yi a cikin kwale-kwalen suna yi domin zuwa gonakansu ko kuma kasuwanni wanda dukka dole ne sai an yi su domin hanyoyi ne na gudanar da rayuwar yau da kullum ta al’umma.

 

Akwai fa yankuna da dama da ke fama da irin wannan matsala ko a Karamar Hukumar Miga akwai mahayin kogi da ke yankin mazabar Sansani da ke fama da irin wannan matsala a duk lokacin damina.

 

Tabbas wannan matsala ta kifewar kwale-kwale matsala ce da ta jima tana faruwa a sassan kananan hukumomi na jiharmu ta Jigawa, duba da yadda wannan matsala take faruwa duk shekara ya kamata gwamnati ta yi dukkanin abin da ya dace domin magance matsalar, tunda babban aikin gwamnati shi ne kare rayukan al’umma da dukiyarsu.

 

Hakika wadanan yankuna da ake fuskantar wannan matsala ta kifewar kwale-kwale suna da matukar tasiri da muhimmanci a tattalin arzikin jiharmu domin yankuna ne da ake noman rani da damina ga kuma sana’ar kamun kifi ko su da kuma kiwon dabobi, don haka sun cancanci a ba su kulawa domin kare rayukan al’umma da dama habaka tattalin arzikin jiharmu.

 

Tabbas ya kamata gwamnati ta yi kokarin hada hannu da jami’an tsaro wajen kula da irin wadanan yankuna da ake tafiye-tafiye a cikin ruwa, domin rage lodin jama’a da kaya da ake yi wa wadanan kwale-kwale da ya yi yawa.

 

Daga karshe nake addu’ar Allah ya yi riko da hannayen Gwamna Malam Umar Namadi Danmodi wajen magance wannan matsala dama gudanar da mulkin jiharmu ta Jigawa don alfarmar Annabin Rahama (S.A.W).

[email protected].

Kifewar kwale-kwale
Leadership Hausa
Website |  + posts Bio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
Kifewar kwale-kwale
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Gwarzo Na Shirin Sake Fitowa Domin Kawo Sabbin Salon Siyasa A Kano
Siyasa

Gwarzo Na Shirin Sake Fitowa Domin Kawo Sabbin Salon Siyasa A Kano

April 25, 2026
Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 
Ra'ayoyi

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

March 18, 2025
Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri
Ra'ayoyi

Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri

November 10, 2024
Next Post
DSS Ta Kama Tsohon Editan BBC, Adejuwon Soyinka A Filin Jirgin Sama Na Legas

DSS Ta Kama Tsohon Editan BBC, Adejuwon Soyinka A Filin Jirgin Sama Na Legas

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.