• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutum 2,629,025 Ke Da Wuƙa Da Namar Zabo Sabon Gwamnan Edo -INEC 

by Yusuf Shuaibu
10 months ago
in Labarai, Siyasa
0
Mutum 2,629,025 Ke Da Wuƙa Da Namar Zabo Sabon Gwamnan Edo -INEC 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta bayyana cewa masu kada kuri’a miliyan 2,629,025 ne za su zabi sabon gwamnan Jihar Edo, a zaben da za a yi a ranar 21 ga watan Satumba.

Kwamishiniyar INEC mai sa ido da ke kula da jihohin Edo, Delta da Kuros Riba, Farfesa Rhoda Gumus, ta bayyana haka a ofishin hukumar da ke Benin a wajen gabatar da rajistar masu kada kuri’a ga shugabanni da wakilan jam’iyyun siyasa 16 da suka shiga zaben.

  • Zaben Ondo: 20 Ga Mayu Ita Ce Ranar Mika Sunayen ‘Yan Takara Ta Karshe – INEC
  • Laifukan Zabe Barazana Ne Ga Samun Sahihan Zabuka A Nijeriya – INEC

Gumus ta ce, “A bisa dokar zabe ta 2022, tilas ne INEC ta gabatar da rajistar masu zabe ga shugabannin jam’iyyun siyasa nan da kwanaki 30 kafin zaben. Muna kokarin bin doka da oda tare da aiwatar da ayyuka 10 cikin 13 da aka shirya gudanarwa a zaben gwamnan Edo.”

Yayin da take jaddada bukatar a gudanar da zaben cikin lumana, Gumus ta ce, “Bai kamata zabe ya zama ko a mutu ko a yi rai ba. Idan ba ku ci nasara ba a yau, kuna iya yin nasara a gobe. Matsaloli kullum suna tashi a ranar zabe. ‘Yan siyasa da magoya bayansu a Jihar Edo su guji tashin hankali.

“INEC ta shirya tsaf domin gudanar da zaben gwamna a Jihar Edo. Muna son masu ruwa da tsaki su bai wa hukumar zabe hadin kai domin ganin ayyukan kafin zabe da lokacin zabe da kuma bayan zabe sun gudana yadda ake bukata. Ina ba da tabbacin cewa tare da goyon bayan jami’an tsaro za a gudanar da zaben cikin kwanciyar hankali da walwala.”

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

Kwamishiniyar ta kasa mai sa ido kuma bukaci mazauna Edo da sauran ‘yan Nijeriya da su yi alfahari da kasarsu, kuma ka da su bari kabila ko harshe ya raba su.

Tun da farko kwamishinan zabe a Jihar Edo, Dakta Anugbum Onuoha, ya sake nanata cewa mutane 2,501,081 ne aka yi wa rajista a jihar domin zaben 2023, yayin da mutane 173,048 suka yi rajista a ci gaba da rajistar masu kada kuri’a daga ranar 27 ga watan Mayu zuwa 9 ga watan Yuni, 2024. Masu rajista 119,206, ciki har da wadanda suka sauya katin zabensu suka cancanta, wanda hakan ya kawo adadin masu kada kuri’a 2,501,081.

Onuoha ya ce za a dakatar da yakin neman zabe a ranar 19 ga watan Satumba, yayin da zaben gwamnan Edo zai gudana a ranar 21 ga watan Satumba.

Shugaban majalisar hadakan jam’iyyu a Edo, Greg Igbinomwanhia, wanda kuma shi ne shugaban jam’iyyar ‘Redemption’ na jihar, ya yaba wa INEC kan yadda ta ke kokarin gudanar da ayyukan zaben ba tare da tangarda ba.

Igbinomwanhia ya kara da cewa zaben gwamnan Jihar Edo da za a yi a ranar 21 ga watan Satumba ba dole ne ya kasance an yi shi cikin ‘yanci da adalci da kuma zaman lafiya.

Ya bukaci shugabanni da magoya bayan jam’iyyun siyasa da su guji tashin hankali domin a zabi magajin Gwamna Godwin Obaseki ba tare da nuna adawa ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ElectionFilatoZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wasu Barayin Shanu Da Hatsabiban ‘Yan Bindiga Sun Shiga Hannu

Next Post

An Cafke Mutumin Da Ake Zargi Da Garkuwa Da Almajirai 2 A Bauchi

Related

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

20 minutes ago
Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 
Siyasa

Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

36 minutes ago
Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu
Labarai

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

3 hours ago
2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu
Siyasa

2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

5 hours ago
Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 
Labarai

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

7 hours ago
Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya
Siyasa

Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

8 hours ago
Next Post
An Cafke Mutumin Da Ake Zargi Da Garkuwa Da Almajirai 2 A Bauchi

An Cafke Mutumin Da Ake Zargi Da Garkuwa Da Almajirai 2 A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

June 29, 2025
Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

June 29, 2025
An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

June 29, 2025
Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

June 29, 2025
Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

June 29, 2025
Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

June 29, 2025
2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

June 29, 2025
Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

June 29, 2025
Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

June 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.