• English
  • Business News
Monday, August 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministan Ma’adanai Ya Bukaci Masu Harkar Ma’adanai A Jihar Nasarawa Su Zauna Lafiya

by Leadership Hausa
11 months ago
in Labaran Kasuwanci
0
Ministan Ma’adanai Ya Bukaci Masu Harkar Ma’adanai A Jihar Nasarawa Su Zauna Lafiya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan ma’aikatar bunkasar harkokin ma’adanaiwta tarayya (ministry of Solid Minerals Development), Dele Alake ya yi kira na musamman ga dukkan hukumomi masu harkokin haka da sarrafa ma’adanai musamman a karamar hukumar Nasarawa da jihar baki daya su zauna lafiya da juna ayayin da suke gudanar da harkokinsu.

Alake ya yi kiran ne jim kadan bayan wani zama na musamman da ya yi da Gwamnan Jihar Nasarawa Injiniya Abdullahi Sule da wasu mukarraban gwamnatinsa a gidan gwamnati da ke birnin Lafiya, fadar jihar ranar Litinin.

  • NNPC Ya Ƙara Farashin Man Fetur Zuwa 855 Kan Kowace Lita 

Dele Alake wanda darakta janar na sashin ma’aikatar da ake kira “Cadastry” a turance ya wakilce shi ya ce ba shakka kiran ya zama wajibi idan aka yi la’akari da mahimmancin zaman lafiya a tsakanin masu harkokin ma’adanan don ta haka ne kawai za su samu ci gaba da bunkasar harkokin nasu a dukkan matakai.
A cewarsa, dole ne hukumomin daban-daban a jihar su hada kai su koma teburin sasantawa don warware duka rigingimu da ke tsakanin su kasancewar sai da zaman lafiya da fahimtar juna tsakanin su kadai hukumomi masu zuba jari daga gida Nijeriya da ƙasashen waje za su samu damar ci gaba da zuba jari a harkokin ma’adanan karamar hukumar ta Nasarawa da jihar baki daya.

Ministan Dele Alake ya kuma yaba wa gwamnan jihar Injiniya Abdullahi Sule dangane da abin da ya bayyana a matsayin gagarumin gudunmawa da gwamnatin sa ke bayarwa a kai-a kai wajen bunkasar harkokin ma’adanan da safarar su a dukkam matakai inda ya ce tabbas hakan ne ma ya aza jihar a mataki na gaba-gaba a ƙasar nan a fannin ci gaba da bunkasar ma’adanan a yanzu haka.

Daganan sai ministan ya kuma yi amfani da wannan damar inda ya sanar cewa tuni ma’aikatarsa ta yanke shawarar gudanar da wani gagarumin taro a watan Nuwambar shekarar 2024 kuma ma’aikatar ta zabi jihar Nasarawa a matsayin wajen da za a gudanar da taron bisa la’akari da gagarumin gudunmawa da take bayarwa wajen bunkasar harkokin ma’adananta da ta ƙasa baki daya.
Da yake jawabi, Gwamna Abdullahi Sule, bayan ya gode wa bakin nasa dangane da ziyarar da kuma zabar jihar tasa a matsayin inda za a gudanar da babban taron ma’adanan ya kuma tabbatar masu da cewa a shirye gwamnatinsa take ta ci gaba da bai wa fannin fifiko kasancewar Allah ya albarkaci jihar da dinbin ma’adanai iri daban-daban.
Sauran manyan baki da suka yi jawabi a yayin ziyarar har da kwamishinan ma’aikatar ma’adanai da albarkatun kasa na jihar ta Nasarawa, Honorabu Kwanta Yakubu inda suka yi fatan alheri da samun nasarorin da ake fatan gani a fannin na ma’adanai.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

Kuratan Sojoji 1,196 Aka Yaye A Makarantar Horar Da Sojoji Ta Zariya


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ci GabaHakar Ma'adanaiMinistaNasarawaZaman Lafiya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mataimakin Shugaban Sin Ya Gana Da Firaministan Jamhuriyar Nijar

Next Post

Dangote Ya Ceto Nijeriya Daga Durƙushewa – Otedola

Related

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025
Labaran Kasuwanci

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

3 weeks ago
Kuratan Sojoji 1,196 Aka Yaye A Makarantar Horar Da Sojoji Ta Zariya
Labaran Kasuwanci

Kuratan Sojoji 1,196 Aka Yaye A Makarantar Horar Da Sojoji Ta Zariya

1 month ago
Za Mu Tabbatar Da Samun Kyakkyawar Alaka Da Gwamnati Don Ci Gaban Kasuwar Kofar Ruwa – ‘Yanleman
Labaran Kasuwanci

Za Mu Tabbatar Da Samun Kyakkyawar Alaka Da Gwamnati Don Ci Gaban Kasuwar Kofar Ruwa – ‘Yanleman

7 months ago
Alternative Bank Shi Ne Mafi Inganci Da Baya Amfani Da Kuɗin Ruwa Da Zuwa Da Fasaha A 2024
Labarai

Alternative Bank Shi Ne Mafi Inganci Da Baya Amfani Da Kuɗin Ruwa Da Zuwa Da Fasaha A 2024

8 months ago
Kamfanin NNPCL Zai Cefanar Da Matatun Mai Na Kaduna Da Warri
Labarai

Kamfanin NNPCL Zai Cefanar Da Matatun Mai Na Kaduna Da Warri

11 months ago
Rikicin Dangote Da NMDPRA: Gwamnatin Tarayya Zata Yi Sasanci
Labaran Kasuwanci

Rikicin Dangote Da NMDPRA: Gwamnatin Tarayya Zata Yi Sasanci

1 year ago
Next Post
Dangote Ya Ceto Nijeriya Daga Durƙushewa – Otedola

Dangote Ya Ceto Nijeriya Daga Durƙushewa - Otedola

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

August 4, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

August 4, 2025
Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

August 4, 2025
Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

August 4, 2025
Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

August 4, 2025
Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa

Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa

August 4, 2025
Gina Tituna A Karkara Yana Bunkasa Tattalin Arziki – Gwamna Sule

Gina Tituna A Karkara Yana Bunkasa Tattalin Arziki – Gwamna Sule

August 4, 2025
Tsohon Dan Majalisar Taraba Usman Ya Fice Daga APC

Tsohon Dan Majalisar Taraba Usman Ya Fice Daga APC

August 4, 2025
Yadda Al’ummar Da Ke Zaune Da ‘Yan Bindiga Ke Rayuwa A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane Da Dama A Kauyukan Zamfara

August 4, 2025
Gwamnatin Kano Za Ta Mayar Da Gidan Gyaran Hali Na Kurmawa Gidan Tarihi

Gwamnatin Kano Za Ta Mayar Da Gidan Gyaran Hali Na Kurmawa Gidan Tarihi

August 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.