ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministan Ma’adanai Ya Bukaci Masu Harkar Ma’adanai A Jihar Nasarawa Su Zauna Lafiya

by Leadership Hausa
2 years ago
ma'adan

Ministan ma’aikatar bunkasar harkokin ma’adanaiwta tarayya (ministry of Solid Minerals Development), Dele Alake ya yi kira na musamman ga dukkan hukumomi masu harkokin haka da sarrafa ma’adanai musamman a karamar hukumar Nasarawa da jihar baki daya su zauna lafiya da juna ayayin da suke gudanar da harkokinsu.

Alake ya yi kiran ne jim kadan bayan wani zama na musamman da ya yi da Gwamnan Jihar Nasarawa Injiniya Abdullahi Sule da wasu mukarraban gwamnatinsa a gidan gwamnati da ke birnin Lafiya, fadar jihar ranar Litinin.

  • NNPC Ya Ƙara Farashin Man Fetur Zuwa 855 Kan Kowace Lita 

Dele Alake wanda darakta janar na sashin ma’aikatar da ake kira “Cadastry” a turance ya wakilce shi ya ce ba shakka kiran ya zama wajibi idan aka yi la’akari da mahimmancin zaman lafiya a tsakanin masu harkokin ma’adanan don ta haka ne kawai za su samu ci gaba da bunkasar harkokin nasu a dukkan matakai.
A cewarsa, dole ne hukumomin daban-daban a jihar su hada kai su koma teburin sasantawa don warware duka rigingimu da ke tsakanin su kasancewar sai da zaman lafiya da fahimtar juna tsakanin su kadai hukumomi masu zuba jari daga gida Nijeriya da ƙasashen waje za su samu damar ci gaba da zuba jari a harkokin ma’adanan karamar hukumar ta Nasarawa da jihar baki daya.

ADVERTISEMENT

Ministan Dele Alake ya kuma yaba wa gwamnan jihar Injiniya Abdullahi Sule dangane da abin da ya bayyana a matsayin gagarumin gudunmawa da gwamnatin sa ke bayarwa a kai-a kai wajen bunkasar harkokin ma’adanan da safarar su a dukkam matakai inda ya ce tabbas hakan ne ma ya aza jihar a mataki na gaba-gaba a ƙasar nan a fannin ci gaba da bunkasar ma’adanan a yanzu haka.

Daganan sai ministan ya kuma yi amfani da wannan damar inda ya sanar cewa tuni ma’aikatarsa ta yanke shawarar gudanar da wani gagarumin taro a watan Nuwambar shekarar 2024 kuma ma’aikatar ta zabi jihar Nasarawa a matsayin wajen da za a gudanar da taron bisa la’akari da gagarumin gudunmawa da take bayarwa wajen bunkasar harkokin ma’adananta da ta ƙasa baki daya.
Da yake jawabi, Gwamna Abdullahi Sule, bayan ya gode wa bakin nasa dangane da ziyarar da kuma zabar jihar tasa a matsayin inda za a gudanar da babban taron ma’adanan ya kuma tabbatar masu da cewa a shirye gwamnatinsa take ta ci gaba da bai wa fannin fifiko kasancewar Allah ya albarkaci jihar da dinbin ma’adanai iri daban-daban.
Sauran manyan baki da suka yi jawabi a yayin ziyarar har da kwamishinan ma’aikatar ma’adanai da albarkatun kasa na jihar ta Nasarawa, Honorabu Kwanta Yakubu inda suka yi fatan alheri da samun nasarorin da ake fatan gani a fannin na ma’adanai.

LABARAI MASU NASABA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Nijeriya Ta Yi Asarar Biliyoyin Naira Saboda Dakatar Da Shigo Da Motoci Ta Iyakokinta

ma'adan
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba
Labaran Kasuwanci

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Nijeriya Ta Yi Asarar Biliyoyin Naira Saboda Dakatar Da Shigo Da Motoci Ta Iyakokinta
Labaran Kasuwanci

Nijeriya Ta Yi Asarar Biliyoyin Naira Saboda Dakatar Da Shigo Da Motoci Ta Iyakokinta

May 29, 2026
Farashin Siminti Zai Ragu Idan Farashin Kayan Aiki Ya Sauka – BUA
Labaran Kasuwanci

Farashin Siminti Zai Ragu Idan Farashin Kayan Aiki Ya Sauka – BUA

May 21, 2026
Next Post
Dangote Ya Ceto Nijeriya Daga Durƙushewa – Otedola

Dangote Ya Ceto Nijeriya Daga Durƙushewa - Otedola

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.