ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, September 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministan Ma’adanai Ya Bukaci Masu Harkar Ma’adanai A Jihar Nasarawa Su Zauna Lafiya

by Leadership Hausa
2 years ago
ma'adan

Ministan ma’aikatar bunkasar harkokin ma’adanaiwta tarayya (ministry of Solid Minerals Development), Dele Alake ya yi kira na musamman ga dukkan hukumomi masu harkokin haka da sarrafa ma’adanai musamman a karamar hukumar Nasarawa da jihar baki daya su zauna lafiya da juna ayayin da suke gudanar da harkokinsu.

Alake ya yi kiran ne jim kadan bayan wani zama na musamman da ya yi da Gwamnan Jihar Nasarawa Injiniya Abdullahi Sule da wasu mukarraban gwamnatinsa a gidan gwamnati da ke birnin Lafiya, fadar jihar ranar Litinin.

  • NNPC Ya Ƙara Farashin Man Fetur Zuwa 855 Kan Kowace Lita 

Dele Alake wanda darakta janar na sashin ma’aikatar da ake kira “Cadastry” a turance ya wakilce shi ya ce ba shakka kiran ya zama wajibi idan aka yi la’akari da mahimmancin zaman lafiya a tsakanin masu harkokin ma’adanan don ta haka ne kawai za su samu ci gaba da bunkasar harkokin nasu a dukkan matakai.
A cewarsa, dole ne hukumomin daban-daban a jihar su hada kai su koma teburin sasantawa don warware duka rigingimu da ke tsakanin su kasancewar sai da zaman lafiya da fahimtar juna tsakanin su kadai hukumomi masu zuba jari daga gida Nijeriya da ƙasashen waje za su samu damar ci gaba da zuba jari a harkokin ma’adanan karamar hukumar ta Nasarawa da jihar baki daya.

ADVERTISEMENT

Ministan Dele Alake ya kuma yaba wa gwamnan jihar Injiniya Abdullahi Sule dangane da abin da ya bayyana a matsayin gagarumin gudunmawa da gwamnatin sa ke bayarwa a kai-a kai wajen bunkasar harkokin ma’adanan da safarar su a dukkam matakai inda ya ce tabbas hakan ne ma ya aza jihar a mataki na gaba-gaba a ƙasar nan a fannin ci gaba da bunkasar ma’adanan a yanzu haka.

Daganan sai ministan ya kuma yi amfani da wannan damar inda ya sanar cewa tuni ma’aikatarsa ta yanke shawarar gudanar da wani gagarumin taro a watan Nuwambar shekarar 2024 kuma ma’aikatar ta zabi jihar Nasarawa a matsayin wajen da za a gudanar da taron bisa la’akari da gagarumin gudunmawa da take bayarwa wajen bunkasar harkokin ma’adananta da ta ƙasa baki daya.
Da yake jawabi, Gwamna Abdullahi Sule, bayan ya gode wa bakin nasa dangane da ziyarar da kuma zabar jihar tasa a matsayin inda za a gudanar da babban taron ma’adanan ya kuma tabbatar masu da cewa a shirye gwamnatinsa take ta ci gaba da bai wa fannin fifiko kasancewar Allah ya albarkaci jihar da dinbin ma’adanai iri daban-daban.
Sauran manyan baki da suka yi jawabi a yayin ziyarar har da kwamishinan ma’aikatar ma’adanai da albarkatun kasa na jihar ta Nasarawa, Honorabu Kwanta Yakubu inda suka yi fatan alheri da samun nasarorin da ake fatan gani a fannin na ma’adanai.

LABARAI MASU NASABA

Wani Kamfani Ya Tallafa Wa Masu Sana’ar Shayi A Kano

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

ma'adan
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja
  • Leadership Hausa
    Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed
  • Leadership Hausa
    Batun Dawo Da Tallafin Mai Da Atiku Ya Yi Na Ci Gaba Da Tayar Da Kura
  • Leadership Hausa
    Batun Guguwar Kakar Yakin Neman Zabukan 2027 A Nijeriya

MASU ALAKA

Wani Kamfani Ya Tallafa Wa Masu Sana’ar Shayi A Kano
Labaran Kasuwanci

Wani Kamfani Ya Tallafa Wa Masu Sana’ar Shayi A Kano

August 23, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba
Labaran Kasuwanci

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Nijeriya Ta Yi Asarar Biliyoyin Naira Saboda Dakatar Da Shigo Da Motoci Ta Iyakokinta
Labaran Kasuwanci

Nijeriya Ta Yi Asarar Biliyoyin Naira Saboda Dakatar Da Shigo Da Motoci Ta Iyakokinta

May 29, 2026
Next Post
Dangote Ya Ceto Nijeriya Daga Durƙushewa – Otedola

Dangote Ya Ceto Nijeriya Daga Durƙushewa - Otedola

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026
Xi Ya Zanta Ta Wayar Tarho Da Firaministan Birtaniya

Xi Ya Zanta Ta Wayar Tarho Da Firaministan Birtaniya

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.