• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Uba Sani Zai Kaddamar Da Kwalejin Koyon Aikin Jinya Da Ungozoma A Pambegua 

by Sulaiman
11 months ago
in Labarai
0
Ruwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

Gwamnatin Jihar Kaduna, karkashin jagorancin Gwamna Uba Sani, ta shirya tsaf don kaddamar da kwalejin koyon aikin jinya da ungozoma da ke karamar hukumar Soba a  yankin Zaria da ke Jihar.

Hakan na kunshe ne acikin wata tattaunawa da manema labarai da shugaban kwalejin, Dakta Yusuf Bello ya yi ranar Litinin, 9 ga watan Satumba, 2024 gabanin kaddamar da Kwalejin a harabar Kwalejin da ke Pambegua.
  • Gine-gine Da Zubar Da Shara A Magudanun Ruwa Ke Haifar Da Ambaliya A Kaduna – Kwamiti
  • Zanga-zanga: Gwamna Uba Sani Ya Musanta Sanya Dokar Hana Fita A Kaduna
Kwalejin Ta Pambegua, daya ce daga cikin sansanonin kwalejojin da ke da babban sansani a Asibitin Dantshoho, a birnin Kaduna, karkashin shugabancin Dakta Yusuf Bello.
Sansanonin Kwalejin sun hada da Kwalejin Koyon aikin jinya ta Asibitin Dantsoho, Tudun wada, da ke cikin birnin Kaduna; Kwalejin Koyon aikin jinya, Kafanchan, da ke kudancin Kaduna, da Kwalejin Koyon aikin jinya, Pambegua da ke yankin Zaria.
Kwalejin ta samu amincewar hukumomin da ke kula da manyan makarantun kiwon lafiya, da hukumar kula da manyan makarantun kimiyya da fasaha (NBTE) don gudanar da karatuttuka a bangaren aikin jinya na shekaru hudu a jere (ND-HND Nursing), ungozoma (Basic Midwifery) da General Nursing.
Dakta Bello ya jinjina wa al’ummar Pambegua bisa namijin kokarinsu da aljihunsu, da karfinsu wajen ganin an samu damar kaddamar da wannan kwalejin a yankinsu, har ta kuma fara aiki.
Shugaban ya kuma sake mika godiyarsa ta musamman ga Gwamna Uba Sani kan kishinsa ga ci gaban al’ummar Kaduna baki daya.
Tun da farko, Hakimin Pambegua, Karfen Dawakin Zazzau, Sufyan Sani Usman, ya jinjina wa Gwamna Uba, bisa kafa irin wannan kwalejin a yankin, inda ya ce, kwalejin ba al’ummar Pambegua kadai ce za ta amfanar ba, har da yankin Zaria da Jihar Kaduna baki daya.
Hakimin ya kuma gode wa Dakta Bello Yusuf wajen ganin wannan Kwalejin ta samu nasarar kafuwa.
Shugaban kwamitin kwalejin koyon aikin jinya da ungozoma da ke Pambegua, Alhaji Haruna Ahmad, ya kuma yaba da irin gudunmawar da al’umma suka bayar, da suka hada da gyare-gyare da kuma sayan kayan aiki domin tabbatar da gudanar da ayyuka a kwalejin.
Ya kuma yabawa gwamnati bisa yadda ta tabbatar da aikin da aka dade ana jira a yankin tare da tabbatar da cewa al’ummar karkara za su ci gajiyar kokarin gwamnati.
Shi ma Akanta Janar na Jihar Kaduna, kuma tsohon shugaban karamar hukuma, Alhaji Bashir Suleiman Zuntu, ya yaba da irin nasarorin da gwamnati ta samu, ya kuma yi fatan samun nasarar gudanar da ayyuka a kwalejin ta Pambegua.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Karatun UngozomaKiwon Lafiya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tallafi: Tinubu Ya Nuna Son Rai Wajen Raba Kayan Abinci – Kwankwaso

Next Post

Nijeriya Ta Samu Lambobin Yabo 7 A Wasannin Nakasassu Ta Bana

Related

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

2 hours ago
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta
Labarai

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

5 hours ago
Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson
Siyasa

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

7 hours ago
An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
Manyan Labarai

An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

8 hours ago
‘Yancin Gashin Kai: Ma’aikatan Kananan Hukumomi Sun Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki
Labarai

‘Yancin Gashin Kai: Ma’aikatan Kananan Hukumomi Sun Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki

10 hours ago
Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu
Rahotonni

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

11 hours ago
Next Post
Nijeriya Ta Samu Lambobin Yabo 7 A Wasannin Nakasassu Ta Bana

Nijeriya Ta Samu Lambobin Yabo 7 A Wasannin Nakasassu Ta Bana

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

July 26, 2025
Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

July 26, 2025
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

July 26, 2025
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

July 26, 2025
Uba Sani

Natijojin Auren Dattijo Ga Budurwa

July 26, 2025
An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

July 26, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)

Dalilan Da Suka Sa Cinikin Bayi Bai Yi Nasara A Arewacin Nijeriya Ba

July 26, 2025
Sin Ta Gudanar Da Gasar Kirkire-kirkire Ta Daliban Kasa Da Kasa A Yankin Afirka Karo Na Farko

Sin Ta Gudanar Da Gasar Kirkire-kirkire Ta Daliban Kasa Da Kasa A Yankin Afirka Karo Na Farko

July 26, 2025
Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.