• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shirin X Space Na LEADERSHIP: Tabbas Gwamnatin Kano Ta Hau Turbar Bunkasa Ilimi – Mahalarta

by Naziru Adam Ibrahim
1 year ago
in Ilimi
0
Dakatar Da Albashin Sabbin Ma’aikatan Kano: Nakasassu Sun Shiga Tsaka-mai-wuya —Zango
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Masu ruwa da tsaki a fannin ilimi sun yaba wa kokarin Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf, wajen inganta bangaren duba da gagarumar nasarar da ake samu biyo bayan ayyana dokar ta baci da ya yi a fannin ilimin jihar.

Sun bayyana hakan ne cikin shirin tattaunawa da LEADERSHIP ta shirya a shafinta na X da akafi sani da twitter inda masu ruwa da tsakin suka yaba da da matakan da gwamnatin ke dauka.

  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Matafiya A Babbar Hanyar Gusau-Funtua
  • Xi Jinping Ya Yi Rangadi A Birnin Baoji Na Lardin Shaanxi Da Birnin Tianshui Na Lardin Gansu

Cikin jawabinta, babbar hadimar Gwamna Abba Kabir Yusuf, kan ilimin Mata  Hajiya Yesmin Mukhtar, ta ce gwamnan ya gyara makarantu da dama da ke cikin halin kaka-ni-ka-yi tare da bude wasu da a da can baya an nuna musu halin ko in kula.

Sauran ci gaban da aka samu kamar yadda sauran masu tofa albarkacin bakinsu irin su tsohon Kwamishinan Ilimi na Jihar Kaduna, Farfesa Usman Moddibo da mai mallakar shafin Arewa Twitter, Malam Abdullahi Nasarawa suka bayyana, akwai kaddamar da manyan ayyuka na gyaran makarantu da kuma inganta kwazazon malamai.

Duk sun yaba wa gwamnatin jihar kan wasu daga cikin jiga-jigan kokarinta na inganta harkar ilimin irin su ware kaso 29 na kasafin jihar ga bangaren ilimi da diban malamai fiye da 5,600 da biyan kudaden jarrabawar WAEC da NECO ga dalibai da bude cibiyoyin samun ilimin zamani na na’ura mai kwakwalwa.

Labarai Masu Nasaba

Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet

Ilimin Fasaha Shi Ne Tafarkin Cire Nijeriya Daga Kangin Fatara – NBTE

Sai dai sun ce duk da haka akwai sauran aiki a gaba wanda idan aka mayar da hankali tabbas za a yi nasarar har karshe.

Shi ma kwamishinan ilimi na Jihar Kano, Alhaji Umar Haruna Doguwa ya bayyana bukatar yaba kokarin da gwamnatin ke yi ta hanyar ba ta duk wani hadin kai da take bukata don samun nasara.

Zuwa yanzu dai, daga cikin gagarumin kokarin da take yi, Gwamnatin Abba Kabir Yusuf ta fitar da fiye da Naira Biliyan 2.7 domin gina ajujuwa 176 da ofisoshi 88 a sassan kananan hukumomin jihar 44.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AbbagwamnatiIlimikanoX Space
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ibtila’in Ambaliyar Ruwa: Halin Da Birnin Maiduguri Ya Tsinci Kansa A Ciki

Next Post

Ƴan Bindiga Sun Tare Hanyar Zamfara, Sun Sace Matafiya 150

Related

Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet
Ilimi

Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet

14 hours ago
Ilimin Fasaha Shi Ne Tafarkin Cire Nijeriya Daga Kangin Fatara – NBTE
Ilimi

Ilimin Fasaha Shi Ne Tafarkin Cire Nijeriya Daga Kangin Fatara – NBTE

1 week ago
Makarantun Da Ba Ƙwararrun Malamai Za Su Rasa Zama Cibiyar Rubuta Jarrabawar NECO
Ilimi

Makarantun Da Ba Ƙwararrun Malamai Za Su Rasa Zama Cibiyar Rubuta Jarrabawar NECO

2 weeks ago
Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe
Ilimi

Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe

3 weeks ago
Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME
Ilimi

Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME

4 weeks ago
ASUU
Ilimi

Malaman Jami’o’i Sun Zama Abin Tausayi —Kungiyar ASUU

4 weeks ago
Next Post
Ƴan Bindiga Sun Tare Hanyar Zamfara, Sun Sace Matafiya 150

Ƴan Bindiga Sun Tare Hanyar Zamfara, Sun Sace Matafiya 150

LABARAI MASU NASABA

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.