• English
  • Business News
Sunday, July 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Da Ya Sa Na Dakatar Da Sanusi A Matsayin Gwamnan CBN – Jonathan

by Abubakar Sulaiman
10 months ago
in Manyan Labarai
0
Dalilin Da Ya Sa Na Dakatar Da Sanusi A Matsayin Gwamnan CBN – Jonathan
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon Shugaban Najeriya, Goodluck Jonathan, a yau Alhamis ya bayyana cewa dakatar da tsohon Gwamnan babban Bankin Najeriya (CBN), Muhammad Sanusi II, ya faru ne saboda wasu laifukan kuɗi ba don batun zargin batan kuɗi da yayi ba.

Jonathan ya bayyana hakan ne a Abuja yayin ƙaddamar da wani littafi da tsohon Ministan Kudi, Dr. Shamsudeen Usman, ya rubuta mai suna “Public Policy and Agent Interests: Perspectives from the Emerging World.”

  • EFCC Ba Ta Taba Gayyato Ni Gabanta Ba – Jonathan
  • Kabilanci Da Magudin Zabe Ke Kassara Samun Shugabanci Nagari – Jonathan

Jonathan ya musanta ikirarin Muhammadu Sanusi na cewa an dakatar da shi ne saboda ya fallasa zargin batan $49.8 biliyan daga asusun gwamnatin tarayya. Ya yi bayanin cewa an dakatar da Sanusi ne bayan tambayar da kwamitin rahoton kudi na Nijeriya (FRC) ya yi kan wasu kashe-kuɗaɗen da ba su dace ba a CBN. Jonathan ya ƙara da cewa, “Akwai matsalolin da suka dace a bincika.”

Tsohon shugaban ya kuma musanta zargin cewa Nijeriya ta rasa wannan adadin kuɗin a lokacin mulkinsa, yana mai cewa kasafin kuɗin ƙasar a wancan lokacin bai wuce ya kai $31.6 biliyan ba kawai, don haka ba zai yiwu a ce $49.8 biliyan sun bace ba tare da an lura ba.

Jonathan ya jaddada cewa bayan binciken kuɗi na PwC, an gano cewa $1.48 biliyan ne ba a bayyana ba, kuma an umurci kamfanin NNPC da ya biya wannan kuɗin cikin Asusun Tarayya. Ya kuma bayyana cewa binciken majalisar dattijai bai gano shaidar batan miliyoyin kuɗaɗen da ake zargi ba.

Labarai Masu Nasaba

Aikin Bututun Gas Na Nijeriya – Morocco Na Ƙara Samun Ci Gaba

Wasu Ma’aikatan Fadar Kano Sun Maka Sarki Sanusi Gaban Kotu

Sanusi, wanda ya halarci taron, ya mayar da martani cikin raha, inda ya kira Jonathan da “Ogana wanda ya kore Ni,” amma Khalifa ya zaɓi ƙin yin tsokaci kan batun. Maimakon haka, ya ja hankalin ƙasar kan amfani da Matatar man fetur ta Dangote yadda ya kamata tare da kauce wa duk wani cikas ga ci gabanta.

An kuma ƙaddamar da Cibiyar Shamsudeen Usman Foundation da kuma wani taron neman taimakon kuɗi don ƙirƙirar Cibiyar Fasahar Artificial Intelligence a yayin taron.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: JonathanMuhammadu Sunusi IIShamsuddeen Muhammad
ShareTweetSendShare
Previous Post

CMG Da Lardin Jiangsu Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Ta Tallata Tamburar Hajojin Lardin

Next Post

Zamfara: Yadda Zargin Juna Da Hannu A Ta’addanci Ya Yi Kamari Tsakanin Dauda Da Matawalle

Related

Aikin Bututun Gas Na Nijeriya – Morocco Na Ƙara Samun Ci Gaba
Kasashen Ketare

Aikin Bututun Gas Na Nijeriya – Morocco Na Ƙara Samun Ci Gaba

1 hour ago
Wasu Ma’aikatan Fadar Kano Sun Maka Sarki Sanusi Gaban Kotu
Manyan Labarai

Wasu Ma’aikatan Fadar Kano Sun Maka Sarki Sanusi Gaban Kotu

4 hours ago
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Kasashen Ketare

‘Mutum Miliyan 14 Na Iya Mutuwa Nan Da 2030 Saboda Janye Tallafin Trump’

6 hours ago
2027: Shugabannin Hamayya Sun Bazama Neman Goyon Baya A Yankunansu
Manyan Labarai

2027: Shugabannin Hamayya Sun Bazama Neman Goyon Baya A Yankunansu

1 day ago
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna
Labarai

Shettima Ya Ziyarci Buhari A Landan Cikin Sirri Don Duba Lafiyarsa

1 day ago
Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa
Kotu Da Ɗansanda

Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa

1 day ago
Next Post
Zamfara

Zamfara: Yadda Zargin Juna Da Hannu A Ta'addanci Ya Yi Kamari Tsakanin Dauda Da Matawalle

LABARAI MASU NASABA

Aikin Bututun Gas Na Nijeriya – Morocco Na Ƙara Samun Ci Gaba

Aikin Bututun Gas Na Nijeriya – Morocco Na Ƙara Samun Ci Gaba

July 13, 2025
Kawu Sumaila Ya Yabi Gwamnatin Kano Kan Goyon Bayan Kirkiro Sabuwar Jihar Tiga

Kawu Sumaila Ya Yabi Gwamnatin Kano Kan Goyon Bayan Kirkiro Sabuwar Jihar Tiga

July 13, 2025
Wasu Ma’aikatan Fadar Kano Sun Maka Sarki Sanusi Gaban Kotu

Wasu Ma’aikatan Fadar Kano Sun Maka Sarki Sanusi Gaban Kotu

July 13, 2025
Cote d’Iboire Ta Amince Da Kafa Bankin Makamashi Na Afirka

Cote d’Iboire Ta Amince Da Kafa Bankin Makamashi Na Afirka

July 13, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

‘Mutum Miliyan 14 Na Iya Mutuwa Nan Da 2030 Saboda Janye Tallafin Trump’

July 13, 2025
Abubuwa 5 da Ya Kamata Ku Sani Game da Wasan Ƙarshe Tsakanin Chelsea Da PSG

Abubuwa 5 da Ya Kamata Ku Sani Game da Wasan Ƙarshe Tsakanin Chelsea Da PSG

July 13, 2025
Abubuwa 10 Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Peter Rufai, Fitaccen Golan Nijeriya

Abubuwa 10 Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Peter Rufai, Fitaccen Golan Nijeriya

July 13, 2025
Dan Gidan Ancelloti Ya Zama Sabon Kocin Botafago FC

Dan Gidan Ancelloti Ya Zama Sabon Kocin Botafago FC

July 13, 2025
NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

July 12, 2025
Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

July 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.