• English
  • Business News
Saturday, September 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ke Janyo Yawaitar Haduran Jiragen Ruwa Da Damina A Nijeriya?

by Rabi'at Sidi Bala
11 months ago
in Labarai
0
Me Ke Janyo Yawaitar Haduran Jiragen Ruwa Da Damina A Nijeriya?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shafin Taskira shafin ne da ya saba zakulo muku batutuwa daban-daban wadanda suka shafi al’umma.

Tsokacinmu na yau zai yi duba ne game da yawan samun jirgin ruwa a Nijeriya, shin me ke kawo hakan? Hassan Tijjani

  • Yawaitar Ambaliyar Ruwa: Ina Mafita?
  • Yadda Bukukuwan Sallah Suka Kasance A Garuruwanmu – Mabiya Taskira

Assalamu Alaikum Warahmatullahi Wabarakatuhu!

Abubuwan da yake kawo yawan haduran jiragen ruwa a Nijeriya shi ne, suna daukar mutane da yawa a cikin jirgin, wato mutanen da yawansu ya fi karfin jirgin kamar misali a ce jirgin da zai dau mutum 20 sai ki ga sun dauki mutum fiye da haka sai su dauki 30 ko ma fiye da haka to kin ga an yi wa jirgin yawa, ya yi nauyin da zai iya nitsewa da mutane a ciki.

Sannan kuma sai yawan ruwa da ake samu da damina ba mu da fadamun ruwa isassu a Nijeriya saboda za ka ga a haka ma ana rufe fadamu ana gidaje a kai to inda mu can zai je sai ruwa ya samu ya tare a waje guda sai ki ga ruwa ya cika sosai to cikar wannan wajen ruwan shima kokiyar ruwa za ta iya tsinkewa ta kifar da jirgi.

Labarai Masu Nasaba

Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

Ilimi Shi Ne Matakin Nasarar Rayuwar Duniya Da Lahira – Yerima Shettima

Abubakar Tijjani

Hadarin jirgin ruwa na faruwa ne saboda matsaloli guda biyar, wannan matsalolin sun hada da:

1. Yanayi

Yanayi wato yana cikin abin da yake janyo wa hadarin jirgin ruwa saboda ruwan sama, in ana ruwa kogi ya kan cika ya batse, hakan zai sanya in ana tafiya a cikin jirgin saboda karfin ruwa sai jirgin ya fara kifewa ko ya lume

2. Ambaliya

Ambaliya a Nijeriyai na daga cikin abin da yake janyo yawan hadarin jirgin ruwa, duba da yanayin rashin magudanar ruwa da ruwa za rika wucewa, da ruwan Dam da ake saki daga kasashrn da muke makotaka da su wanda yake ratsa gonaki don samun wurin wucewa zuwa kogi, karfin ruwan da yawansa ya kan saka jirgi ya kife, misali, ambaliyar da aka yi a Borno.

3. Rashin ba wa jirgin kulawa wajen gyara

Wannan wata matsala ce da kan iya haifar da faruwar jirgi ya karye ko ya ruguje in an hau, musamman in an masa nauyi

4. Gudu

Gudu na cikin abin da ke janyo yawan hadari a jirgin ruwa, in ana gudu a jirgin ruwa, jirgin ya kan zama bashi da nauyi wanda dan juyi za’a yi kadan ya saka jirgin ya kife

5.Rashin iyawa/Operator inedperience

Rashin gogewa kan tuka jirgin rawa kan haifar da matsaloli da dama kamar jirgi ya kife, jirgi ya tsaya a tsakiyar ruwa, jirgi ya nitse da sauransu.

Rabi’atu Abdullahi Muhammad

To abin da yake janyo hadarin jirgin ruwa shi ne, rashin isassun wajen da ruwa zai tsaya wato fadamomi sun yi kadan kasancewar yawanci ana rufe fadama a yi gida a kai to da zarar an yi ruwan sama sai yabi daji ya shiga kogi, sannan ga Dam shima idan ya cika suka ga zai musu barna suma su sake shi to dagana kogi ya cika to wannan ma zai iya kawo hadarin jirgin ruwa.

Sannan suma masu jirgin ruwan da kansu su kan zama sanadiyar yi saboda daukan mutanan da su kafi yawan da aka tsara jirgin zai dauka kamar idan zai dau mutum goma sai a sama masa 20 ko fiye da haka to da zarar jirgin ya yi kasa dama gashi kogi ya cika abu kadan ne sai ki ga hatsri ya faru wanda za ki ga wani tsabar ya yi nauyi na ciki suna saka hannunsu cikin ruwan saboda ya yi kasa suna ciki suna dan ban ruwan.

Muhammad Abdullahi

Assalamu alaikum!

Abubawan da yake kawo hadarin jirgin ruwa su ne, rashin isassun jirage ko na ce rashin jirage masu kyau, ko kuma rashin kulawa da su akai-akai, sannan sai daukar mutane da yawa wadanda suka fi karfin jirgin, sannan sai cikar ruwa da damina ruwa ya cika ya yi karfi sosai, to idan kokiyar ruwa ta tsinke jirgi na saman ruwa to za ta iya nitsar da shi. To abubuwan dai da yawa ga su duka sai dai Allah ya kara tsarewa.

Habiba Tijjani

Assalamu alaikum!

Abubuwan da suke kawo hadarin jirgin ruwa a Nijeriyai suna da yawa:

Samun ruwan sama mai yawa da damina saboda idan aka samu ruwa sosai da damina kogi zai cika duba da karancin wurin da ruwa yake zama dole kogi yake tafiya, sannan kuma muna da Dam suma can idan suka cika suka ga zai musu barna sakin sa suke yi imma ya yi kogi ko ya yi gari to wannan ya kan janyo hadarin jirgin ruwa saboda kogi ya cika ruwa ya yi karfi.

Sannan sai hada ma ta masu jiragen ruwan ba za su dauki mutane daidai yadda aka ce jirgin zai dauka ba sai sun yi kari sun dauka da yawa to nauyi ma yana iya kawo hadarin jirgin ruwa saboda jirgin zai yi kasa sosai yana tangal-tangal. Allah ya kawo mana sauki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Boat mishapsKogiRuwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murna Ga Sabon Shugaban Kasar Habasha

Next Post

Sin Za Ta Samar Da Karin Matakai Daban Daban Na Tallafawa Tattalin Arziki

Related

Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno
Labarai

Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

32 seconds ago
Labarai

Ilimi Shi Ne Matakin Nasarar Rayuwar Duniya Da Lahira – Yerima Shettima

3 hours ago
NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai
Manyan Labarai

NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai

3 hours ago
Maulidi: Gwamnan Zamfara Ya Taya Al’ummar Musulmi Murna, Ya BuÆ™aci A Dage Da Addu’o’in Samun Zaman Lafiya
Labarai

Maulidi: Gwamnan Zamfara Ya Taya Al’ummar Musulmi Murna, Ya BuÆ™aci A Dage Da Addu’o’in Samun Zaman Lafiya

7 hours ago
Za Mu RiÆ™e Wa Minista Tijjani MuÆ™aminsa Bayan HamÉ“arar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 
Labarai

Ana Ci Gaba Da Caccakar El-rufai Kan Kalamansa Game Da Tsaron Kasa

16 hours ago
Yadda Al’ummar Da Ke Zaune Da ‘Yan Bindiga Ke Rayuwa A Zamfara
Labarai

Duk Da Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ana Ci Gaba Da Kai Hare-hare Wasu Yankunan Zamfara

17 hours ago
Next Post
Sin Za Ta Samar Da Karin Matakai Daban Daban Na Tallafawa Tattalin Arziki

Sin Za Ta Samar Da Karin Matakai Daban Daban Na Tallafawa Tattalin Arziki

LABARAI MASU NASABA

Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

September 6, 2025
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

Kungiyoyi Da Abokan Arziki Na Ci Gaba Da Taya Dantsoho Murna

September 6, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

September 6, 2025
Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

September 6, 2025

Ilimi Shi Ne Matakin Nasarar Rayuwar Duniya Da Lahira – Yerima Shettima

September 6, 2025
NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai

NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai

September 6, 2025
Maulidi: Gwamnan Zamfara Ya Taya Al’ummar Musulmi Murna, Ya BuÆ™aci A Dage Da Addu’o’in Samun Zaman Lafiya

Maulidi: Gwamnan Zamfara Ya Taya Al’ummar Musulmi Murna, Ya BuÆ™aci A Dage Da Addu’o’in Samun Zaman Lafiya

September 6, 2025
Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

September 5, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

September 5, 2025
Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

September 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.