• English
  • Business News
Saturday, July 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ke Janyo Yawaitar Haduran Jiragen Ruwa Da Damina A Nijeriya?

by Rabi'at Sidi Bala
9 months ago
in Labarai
0
Me Ke Janyo Yawaitar Haduran Jiragen Ruwa Da Damina A Nijeriya?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shafin Taskira shafin ne da ya saba zakulo muku batutuwa daban-daban wadanda suka shafi al’umma.

Tsokacinmu na yau zai yi duba ne game da yawan samun jirgin ruwa a Nijeriya, shin me ke kawo hakan? Hassan Tijjani

  • Yawaitar Ambaliyar Ruwa: Ina Mafita?
  • Yadda Bukukuwan Sallah Suka Kasance A Garuruwanmu – Mabiya Taskira

Assalamu Alaikum Warahmatullahi Wabarakatuhu!

Abubuwan da yake kawo yawan haduran jiragen ruwa a Nijeriya shi ne, suna daukar mutane da yawa a cikin jirgin, wato mutanen da yawansu ya fi karfin jirgin kamar misali a ce jirgin da zai dau mutum 20 sai ki ga sun dauki mutum fiye da haka sai su dauki 30 ko ma fiye da haka to kin ga an yi wa jirgin yawa, ya yi nauyin da zai iya nitsewa da mutane a ciki.

Sannan kuma sai yawan ruwa da ake samu da damina ba mu da fadamun ruwa isassu a Nijeriya saboda za ka ga a haka ma ana rufe fadamu ana gidaje a kai to inda mu can zai je sai ruwa ya samu ya tare a waje guda sai ki ga ruwa ya cika sosai to cikar wannan wajen ruwan shima kokiyar ruwa za ta iya tsinkewa ta kifar da jirgi.

Labarai Masu Nasaba

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

Abubakar Tijjani

Hadarin jirgin ruwa na faruwa ne saboda matsaloli guda biyar, wannan matsalolin sun hada da:

1. Yanayi

Yanayi wato yana cikin abin da yake janyo wa hadarin jirgin ruwa saboda ruwan sama, in ana ruwa kogi ya kan cika ya batse, hakan zai sanya in ana tafiya a cikin jirgin saboda karfin ruwa sai jirgin ya fara kifewa ko ya lume

2. Ambaliya

Ambaliya a Nijeriyai na daga cikin abin da yake janyo yawan hadarin jirgin ruwa, duba da yanayin rashin magudanar ruwa da ruwa za rika wucewa, da ruwan Dam da ake saki daga kasashrn da muke makotaka da su wanda yake ratsa gonaki don samun wurin wucewa zuwa kogi, karfin ruwan da yawansa ya kan saka jirgi ya kife, misali, ambaliyar da aka yi a Borno.

3. Rashin ba wa jirgin kulawa wajen gyara

Wannan wata matsala ce da kan iya haifar da faruwar jirgi ya karye ko ya ruguje in an hau, musamman in an masa nauyi

4. Gudu

Gudu na cikin abin da ke janyo yawan hadari a jirgin ruwa, in ana gudu a jirgin ruwa, jirgin ya kan zama bashi da nauyi wanda dan juyi za’a yi kadan ya saka jirgin ya kife

5.Rashin iyawa/Operator inedperience

Rashin gogewa kan tuka jirgin rawa kan haifar da matsaloli da dama kamar jirgi ya kife, jirgi ya tsaya a tsakiyar ruwa, jirgi ya nitse da sauransu.

Rabi’atu Abdullahi Muhammad

To abin da yake janyo hadarin jirgin ruwa shi ne, rashin isassun wajen da ruwa zai tsaya wato fadamomi sun yi kadan kasancewar yawanci ana rufe fadama a yi gida a kai to da zarar an yi ruwan sama sai yabi daji ya shiga kogi, sannan ga Dam shima idan ya cika suka ga zai musu barna suma su sake shi to dagana kogi ya cika to wannan ma zai iya kawo hadarin jirgin ruwa.

Sannan suma masu jirgin ruwan da kansu su kan zama sanadiyar yi saboda daukan mutanan da su kafi yawan da aka tsara jirgin zai dauka kamar idan zai dau mutum goma sai a sama masa 20 ko fiye da haka to da zarar jirgin ya yi kasa dama gashi kogi ya cika abu kadan ne sai ki ga hatsri ya faru wanda za ki ga wani tsabar ya yi nauyi na ciki suna saka hannunsu cikin ruwan saboda ya yi kasa suna ciki suna dan ban ruwan.

Muhammad Abdullahi

Assalamu alaikum!

Abubawan da yake kawo hadarin jirgin ruwa su ne, rashin isassun jirage ko na ce rashin jirage masu kyau, ko kuma rashin kulawa da su akai-akai, sannan sai daukar mutane da yawa wadanda suka fi karfin jirgin, sannan sai cikar ruwa da damina ruwa ya cika ya yi karfi sosai, to idan kokiyar ruwa ta tsinke jirgi na saman ruwa to za ta iya nitsar da shi. To abubuwan dai da yawa ga su duka sai dai Allah ya kara tsarewa.

Habiba Tijjani

Assalamu alaikum!

Abubuwan da suke kawo hadarin jirgin ruwa a Nijeriyai suna da yawa:

Samun ruwan sama mai yawa da damina saboda idan aka samu ruwa sosai da damina kogi zai cika duba da karancin wurin da ruwa yake zama dole kogi yake tafiya, sannan kuma muna da Dam suma can idan suka cika suka ga zai musu barna sakin sa suke yi imma ya yi kogi ko ya yi gari to wannan ya kan janyo hadarin jirgin ruwa saboda kogi ya cika ruwa ya yi karfi.

Sannan sai hada ma ta masu jiragen ruwan ba za su dauki mutane daidai yadda aka ce jirgin zai dauka ba sai sun yi kari sun dauka da yawa to nauyi ma yana iya kawo hadarin jirgin ruwa saboda jirgin zai yi kasa sosai yana tangal-tangal. Allah ya kawo mana sauki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Boat mishapsKogiRuwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murna Ga Sabon Shugaban Kasar Habasha

Next Post

Sin Za Ta Samar Da Karin Matakai Daban Daban Na Tallafawa Tattalin Arziki

Related

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya
Labarai

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

5 hours ago
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano
Labarai

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

6 hours ago
Kasar Sin Ta Nuna Alhinin Rasuwar Tsohon Shugaban Nijeriya Buhari
Labarai

Za A Dinga Tunawa Da Buhari A Matsayin Waliyyi A Siyasar Nijeriya —Dakta Zangina

7 hours ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

Tinubu Ya Nada Ɗan Babangida A Matsayin Shugaban Bankin Manoma

7 hours ago
‘Yan Kasuwa Na Shirin Yi Wa Dangote Zanga-zanga Kan Rage Farashin Gas
Labarai

‘Yan Kasuwa Na Shirin Yi Wa Dangote Zanga-zanga Kan Rage Farashin Gas

8 hours ago
Lai Ching-Te Bai Cancanci Zama Jagoran Yankin Taiwan Ba
Ra'ayi Riga

Lai Ching-Te Bai Cancanci Zama Jagoran Yankin Taiwan Ba

8 hours ago
Next Post
Sin Za Ta Samar Da Karin Matakai Daban Daban Na Tallafawa Tattalin Arziki

Sin Za Ta Samar Da Karin Matakai Daban Daban Na Tallafawa Tattalin Arziki

LABARAI MASU NASABA

Dangote

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

July 18, 2025
Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

July 18, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

July 18, 2025
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

July 18, 2025
majalisar kasa

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

July 18, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

July 18, 2025
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

July 18, 2025
A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

July 18, 2025
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

July 18, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

July 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.