• English
  • Business News
Sunday, October 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Yi Artabu Da Masu Garkuwa Da Mutane A Abuja

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
Artabu

Jami’an rundunar ‘yansandan Babban Birnin Tarayya Abuja sun kama wani da ake zargin mai garkuwa da mutane ne bayan wani kazamin fada da suka yi da ‘yan bindiga.

Wasu gungun masu garkuwa da mutane sun kai farmaki wani gida a unguwar Kubwa da ke Babban Birnin Tarayya Abuja da sanyin safiya bayan da suka gamu da ‘yansanda, inda suka bude wuta tare da gudu zuwa wata fadama da ke kusa.

  • Gwamnatin Tarayya Da Google Sun Bullo Da Hanyar Samar Wa Da Matasa 2,500 Aikin Dogaro Da Kai
  • Tsohon Shugaban INEC, Farfesa Humphrey Nwosu Ya Rasu

Wakilinmu ya ruwaito cewa ‘yansandan sun bi sawun barayin, inda suka kama daya daga cikinsu tare da kwato wata motar gungun barayin.

Da aka tuntubi kwamishinan ‘yan sandan Babban Birnin Tarayya Abuja, Tunji Disu, ya tabbatar da cewa an kama daya daga cikin masu garkuwa da mutanen tare da kwace makamin dake hannunsa.

Ya ce ‘yan sandan sun yi gaggawar kai dauki ne saboda kiran da daya daga cikin mazauna yankin ya yi.

LABARAI MASU NASABA

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

Disu ya bukaci mazauna yankin da su gaggauta tuntubar layukan gaggawa na rundunar a duk lokacin da suka ga abubuwan da ba su dace ba a muhallinsu.

Ya ce, “An yi sa’a an kama daya daga cikinsu, wasu kuma sun tsere. Sannan kuma mun kwato musu bindiga kirar AK-47 da harsashi mai rai guda 20, da bindigar Beretta da harsashi 12 a cikinta.

“Muna kokarin kama wasu da suka tsere. Yana da mahimmanci a lura cewa muna so mu gode wa wadanda suka ga lamarin kuma suka kira ‘yan sanda da sauri.

Muna rokon jama’a kada su tsaya jira yayin da suka ga wani da zai kawo rashin zaman lafiya ba tare da daukar mataki ba. Su yi la’akari da duk wani mataki da ke faruwa, da zarar sun ga wani yanayi da ya yi kama da fashi, su kira shashen gaggawa ‘yan sanda za su kawo daukin gaggawa.

“Don haka ina so in gode wa wanda ya kira mu mu dauki matakin gaggawa. Zan yi iyakacin kokarina domin nemo wadanda da suka tsere daga wurin da lamarin ya faru don neman mafaka. “

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi
Kotu Da Ɗansanda

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

October 4, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

October 4, 2025
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Farmaki Masu Safarar Muggan Kwayoyi A Sassan Nijeriya

September 27, 2025
Next Post
Wani Mutum Ya Kashe Kishiyar Mahaifiyarsa A Kogi

An Cafke Wasu Matasa Da Laifin Fashin Wayoyi A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Abin Da Ya Sa Aka Yi Watsi Da Tashar Jiragen Ruwa Ta Kan Tudu Da Ke Jihar Kaduna

Abin Da Ya Sa Aka Yi Watsi Da Tashar Jiragen Ruwa Ta Kan Tudu Da Ke Jihar Kaduna

October 26, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Kama Wasu Mutum Biyu Da Ake Zargi Da Haɗa Baki Da ‘Yan Bindiga A Kano

October 26, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwamnatin Kaduna Tare Da  AUDA–NEPAD Sun Tallafa Wa Manoma 400 Da Kayan Noma

October 26, 2025
Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

October 26, 2025
Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025 Kamfanin GEIL

Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025 Kamfanin GEIL

October 26, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Ɗan Majalisa Na Shekarar 2025: Benjamin Okezie Kalu

October 26, 2025
An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 25, 2025

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

October 25, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Banki Na Shekarar 2025 Bankin Providus

October 25, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.