• English
  • Business News
Tuesday, July 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Cafke Wasu Matasa Da Laifin Fashin Wayoyi A Bauchi

by Rabi'u Ali Indabawa
9 months ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
Wani Mutum Ya Kashe Kishiyar Mahaifiyarsa A Kogi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar ‘yan sandan Jihar Bauchi ta ce ta kama wasu yara matasa biyu da laifin yin fashi a wani kantin sayar da wayar salula guda 100 da na’urar jin waka guda 75 da dai sauransu.

Kakakin rundunar ‘yan sandan, Ahmed Wakil, a wata sanarwa da ya fitar ya bayyana cewa aikin kamen ya biyo bayan rahoton sata da mai shagon ya kai.

  • NSCDC Ta Cafke Hatsabibin Ɗan Bindiga A Kano
  • Kashi 4.1 Na ‘Yan Nijeriya Ne Kawai Za Su Amfana Da Tsarin Mafi Karancin Albashi —Bankin Duniya

Ya kuma jaddada cewa da samun rahoton ne jami’an ‘yan sanda suka fara gudanar da bincike a kan lamarin, wanda ya kai ga cafke wasu dalibai biyu na makarantar sakandare ta Bakari Dukku.

PPRO ya kara da cewa da aka kama wadanda ake zargin, suka amsa cewa sun samu makullin kantin ne daga inda mai shagon ya ajiye.

Wadanda ake zargin sun kuma bayyana wa ‘yan sanda cewa sun sayar da wasu daga cikin wayoyin kan kudi Naira 5,000 da Naira 8,000.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Damke Mutum Shida Kan Kisan Da Aka Yi A Kasuwar Abuja

Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa

Wakil ya bayyana cewa, “Da samun rahoton, kwamishinan ‘yan sandan ya umurci tawagar ORP karkashin jagorancin CSP Kim Albert da su gudanar da bincike. Binciken ya kai ga cafke Hamza Sadik, namiji mai shekaru 15 da Adamu Ahmadu, mai shekaru 15. Dukkanin mutanen biyu daliban makarantar sakandaren Bakari Dukku ne.

“Lokacin da ake yi masa tambayoyi, wadanda ake zargin sun amsa cewa sun samu nasarar samun makullin shagon ne daga inda aka boye shi, sannan suka tsayar da lokacin da mai shagon zai tafi kasuwar kauyen, sannan suka bude kofar shagon domin yin sata da rana.

“Wadanda ake zargin sun sayar da kayayyakin da aka sace a kan farashi mai rahusa, daga Naira 8,000 zuwa Naira 5,000. An yi amfani da kudaden da aka samu wajen sayan tufafi, abinci, da wayar salula, wanda daga baya kuma aka sace wasu kayan daga hannun daya daga cikin wadanda ake zargin.”

Ya kara da cewa wasu daga cikin abubuwan da aka sace sun hada da “wayoyin hannu 21, MP4 MP4, caja daya, da makullin karfe daya, daga hannun wadanda ake zargin.”

Yayin da yake jaddada kudirin rundunar ta yaki da miyagun laifuka, Wakil ya ce za a mika wadanda ake zargin zuwa gidan kaso domin gyaran hali bayan kammala binciken da ake yi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BauchiLaifiMatasa
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yansanda Sun Yi Artabu Da Masu Garkuwa Da Mutane A Abuja

Next Post

Mun Ƙudiri Nema Wa Arewa Mafita – Shekarau

Related

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Damke Mutum Shida Kan Kisan Da Aka Yi A Kasuwar Abuja

3 days ago
Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa
Kotu Da Ɗansanda

Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa

3 days ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

1 week ago
‘Yan Sanda Sun Kama Mutum 2 Kan Zargin Jefe Wani Direba Har Lahira A Ondo
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona

2 months ago
Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe
Kotu Da Ɗansanda

Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

2 months ago
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi

3 months ago
Next Post
Mun Ƙudiri Nema Wa Arewa Mafita – Shekarau

Mun Ƙudiri Nema Wa Arewa Mafita - Shekarau

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

July 15, 2025
An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing

An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing

July 15, 2025
Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%

Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%

July 15, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato

July 15, 2025
Shugaba Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Game Da Aikin Raya Birane 

Shugaba Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Game Da Aikin Raya Birane 

July 15, 2025
Ƴansanda Sun Cafke Mutane Biyu Bisa Zargin Kashe Ɗan Ƙasar China

Ƴansanda Sun Cafke Mutane Biyu Bisa Zargin Kashe Ɗan Ƙasar China

July 15, 2025
Taron Matasan Sin Da Afrika Kan Tsaro Zai Kirkiro Wata Sabuwar Mahanga Ta Magance Matsalolin Tsaro

Taron Matasan Sin Da Afrika Kan Tsaro Zai Kirkiro Wata Sabuwar Mahanga Ta Magance Matsalolin Tsaro

July 15, 2025
Girman Kai Da Son Zuciya Ba Za Su Sa A Amince Ko Ba Da Hadin Kai Ba

Girman Kai Da Son Zuciya Ba Za Su Sa A Amince Ko Ba Da Hadin Kai Ba

July 15, 2025
Bayan Shekaru 6 A Hannun Boko Haram, Wasu Yara Biyu Sun Kuɓuta

Bayan Shekaru 6 A Hannun Boko Haram, Wasu Yara Biyu Sun Kuɓuta

July 15, 2025
Mai Gaskiya Ya Koma Gida: Za A Yi Jana’izar Buhari A Daura

Mai Gaskiya Ya Koma Gida: Za A Yi Jana’izar Buhari A Daura

July 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.