• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kaddamar Da Cibiyar ‘Yan Jarida Ta Afirka Masu Amfani Da Harshen Hausa A Nijar

by Muhammad Bashir and Sulaiman
8 months ago
in Labarai
0
Jarida
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kokarin da ake na bunkasa ayyukan ‘yan jarida masu amfani da harshen Hausa a Nahiyar Afrika, an kaddamar da cibiyar kungiyar a birnin Niamey na Jamhuriyar Nijar.

Wannan ne karo na farko da aka samar da irin wannan kungiya bisa la’akari da jajircewar da ake yi na ganin an bunkasa harsunan cikin gida musamman Hausa, wanda yake kokarin mamaye sauran harsuna a Nahiyar Afrika.

  • Majalisar Wakilai Ta Gabatar Da Kudirin Kara Yawan Membobi Daga 360 Zuwa 366
  • Rikicin Jam’iyyar NNPP Ya Kazanta A Kano

A yayin kaddamar da cibiyar kungiyar tare da kwarkwaryar zantawa da ‘yan jaridu na kasa da kasa, da sauran wakilai da suka zo daga sassa daban-daban ciki har da Nijeriya, masu ruwa da tsaki a wannan taro sun bayyana muhimmancin wannan kungiya wadda take da manufar aiwatar da aikin jarida nagartacce musamman zaburar da jama’a kan muhimmancin gina al’umma da samar da ci gaba mai dorewa.

 

Maryam Sarki Azbin, wadda ta zama jigo wajen samar da wannan kungiya, ta ce lokaci ya yi da za a rika amfani da harshen cikin gida wajen isar da muhimman sakonni ga al’umma a duk inda suke.

Labarai Masu Nasaba

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Sarki Azbin ta bukaci ‘yan jarida da su kauce wa abubuwan da suke bata wa aikinsu kima a idon jama’a kamar izgilanci, da maula, da kwadayi, da bambadanci da keta mutuncin masu fada a ji.

Ta kara da cewa, kungiyar ta ‘yan jarida za ta yi dukkan mai yiwa wajen zaburar da ‘yan jaridu kan yadda za su rika amfani da harshen Hausa wajen sanar da mutane abubuwan da za su amfane su a rayuwarsu ta yau da kullum.

A jawabinsa, shugaban hukumar gidan telebijin da radiyo na jamhuriyar Nijar, RTN, Abdoulaye Koulibaly ya bayyana cewa aikin jarida aiki ne da yake bukatar gaskiya da sanin makamar aiki, don haka kuskure ne ‘yan jarida suke yi wajen ba da labarai na shaci-fadi don son abin hannu wasu masu fada a ji, ko kuma nuna bangaranci yayin fitar da labarai.

Koulibali ya ce samar da wannan kungiya wata dama ce da za ta taimaka wajen magance kalubalen da ‘yan jarida suke fuskanta ta fannin gudanar da ayyukansu, musamman wajen amfani da harshe na cikin gida.

Sauran wadanda suka yi jawabi a wurin sun gamsu da tsare-tsare da manufofin da aka gina kungiyar a kan su, musamman tabbatar da hadin kai da mu’amala a tsakanin ‘yan jarida na kasashe 11 da ke Nahiyar Afrika, suna masu cewa yawan da ‘yan jaridar Hausa da ake da su a Nihiyar sun isa su taka gagarumar gudunmawa wajen magance kalubalen da ake fuskanta, da kuma karfafawa masu kwarin giwa wajen ganin sun yi abin da ya dace na kyautata rayuwar al’ummar yankin.

Shi ma a nasa bangaren, ma’aikaci a hukumar telebijin a tarayyar Nijeriya (NTA), Aliyu Rabe Aliyu ya ce, babban aikin da kungiyar ‘yan jarida masu amfani da harshen Hausa za ta sa a gaba shi ne, sauya fasalin aikin jaridar gado na ‘yan ku ci ku ba mu, ya zuwa aikin jarida na samar da mafita ga tulin kalubalen da yankin yake fuskanta ta hanyar amfani da harshen da kowa yake sonsa, kuma yake amfani da shi watau harshen Hausa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ofishin Jakadancin Faransa Da Hadin Gwiwar IITA Sun Horar Da Mata 500 Kasuwancin Noma

Next Post

‘Yan Nijeriya Miliyan 33 Na Iya Fuskantar Matsalar Rashin Abinci A 2025 —Rahoto

Related

Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25
Labarai

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

56 minutes ago
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

1 hour ago
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)
Labarai

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

2 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

3 hours ago
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

5 hours ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

6 hours ago
Next Post
‘Yan Nijeriya Miliyan 1.8 Ne Ke Fama Da Matsalar Yunwa – Hukumar FAO

‘Yan Nijeriya Miliyan 33 Na Iya Fuskantar Matsalar Rashin Abinci A 2025 —Rahoto

LABARAI MASU NASABA

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

June 28, 2025
Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

June 28, 2025
Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.