• English
  • Business News
Saturday, August 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kori Tsohon Manajan Banki Bisa Zargin Damfarar Naira Miliyan 122

by Rabi'u Ali Indabawa
8 months ago
in Labarai
0
An Kori Tsohon Manajan Banki Bisa Zargin Damfarar Naira Miliyan 122
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata kotun hukunta manyan laifuka ta Jihar Legas da ke Ikeja ta gurfanar da wani tsohon manajan banki reshen Iju, Abiodun Sanni, a gidan yari bisa zargin damfarar Naira miliyan 122,011,441.

Hukumar Yaki Da Masu Yi Wa Tattalin Arzikin Kasa Zagon Kasa, ta gurfanar da Sanni a gaban kuliya 16 da suka hada da karbar bashi ta hanyar karya, amfani da takardun karya da kuma sata.

  • Bankin Duniya Da IMF Na Kassara Tsarin Ilimin Jami’o’i A Nijeriya – ASUU
  • Karancin Kudin Shiga Ya Jefa ‘Yan Nijeriya Miliyan 14 Cikin Kangin Talauci – Bankin Duniya

Lauyan masu shigar da kara na EFCC, O. Adewunmi, ya shaida wa kotun cewa Sanni ya aikata laifin ne a ranar 24 ga Fabrairu, 2020, a Legas.

Adewunmi ya shaida wa kotun cewa wanda ake kara a lokacin yana manajan bankin Polaris Bank Limited reshen lju, ya samu rance ne a matsayin rancen kudi Naira miliyan 17, kan wani Bamgbose Tayo Taofia da ke kasuwanci da suna da salon Banut Haulage. .

Mai gabatar da kara ya bayyana cewa, an samu kudin ne daga bankin Polaris Bank Limited, ta hanyar karyar cewa bashin na da garantin ne a wani kayyade a asusun ajiya mai lamba 0071572791, kudin da ya kai Naira miliyan 111,540,380.52 mallakin Yinkus Multibiz Bentures da kuma mai ita, daya Misis Olayinka. Hannah Aderibigbe, ta amince a yi amfani da shi a matsayin jingina.

Labarai Masu Nasaba

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

Haka kuma an zarge shi da rashin gaskiya da canza wani asusun ajiya na Polaris Bank Limited mai lamba 0071277522 akan kudi Naira miliyan 15, 011,441.00 (Miliyan Goma Sha Biyar, Dubu Sha daya, Dari Hudu da Arba’in da Daya) mallakar Atolagbe Joshua Tinuoye, zuwa amfani da shi.

Sai dai wanda ake tuhumar ya ki amsa laifin da ake tuhumarsa da shi.

Lauyan mai gabatar da kara, ya bukaci kotun da ta ci gaba da tsare wanda ake kara a gidan gyaran hali, har zuwa lokacin da za a fara shari’a.

“Ya Ubangiji, mai gabatar da kara ya yi niyyar gabatar da shaidu 10 game da wannan shari’a kuma muna rokon kotu ta tsare wanda ake kara a gidan yari”, in ji Adewunmi.

Sai dai lauyan da ake kara, Osho Oludoshu, ya shaida wa kotun cewa ya shigar da bukatar neman beli a madadin wanda yake karewa.

A wani takaitaccen hukunci mai shari’a Olubunmi Abike-Fadipe, ta dage ci gaba da sauraron karar tare da bayar da umarnin mika bukatar belin ga kotu kafin ranar da za a fara shari’ar.

“Na dage shari’ar zuwa Match 6 da 19, 2025, kuma na tsare wanda ake kara a gidan gyaran hali. Suna da damar gabatar da takardar neman beli kafin ranar shari’arsa,” in ji alkalin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Banki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotun Birtaniya Ta Daure Wasu ‘Yan Nijeriya 4

Next Post

Dalilin Da Ya Sa Farashin Wake Ba Zai Sauka Ba A Nijeriya -Masana

Related

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Labarai

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

3 hours ago
Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

4 hours ago
Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Barazanar ɗorewar Wutar Lantarki A Nijeriya – Minista
Labarai

Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Barazanar ɗorewar Wutar Lantarki A Nijeriya – Minista

9 hours ago
GORON JUMA’A 01-07-2025
Labarai

GORON JUMA’A 01-07-2025

11 hours ago
An Zaɓi Saidu Yahya A Matsayin Shugaban Hukumar Yaƙi Da Cin Hanci Ta Kano
Manyan Labarai

An Zaɓi Saidu Yahya A Matsayin Shugaban Hukumar Yaƙi Da Cin Hanci Ta Kano

12 hours ago
Shekara 2 Ta Gwamnatin Tinubu: Gwamnonin Arewa Sun ƙaryata Zargin ACF Na Watsi ɗa Yankin
Manyan Labarai

Shekara 2 Ta Gwamnatin Tinubu: Gwamnonin Arewa Sun ƙaryata Zargin ACF Na Watsi ɗa Yankin

14 hours ago
Next Post
Dalilin Da Ya Sa Farashin Wake Ba Zai Sauka Ba A Nijeriya -Masana

Dalilin Da Ya Sa Farashin Wake Ba Zai Sauka Ba A Nijeriya -Masana

LABARAI MASU NASABA

Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa

Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa

August 1, 2025
Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

August 1, 2025
2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

August 1, 2025
Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

August 1, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

August 1, 2025
Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

August 1, 2025
Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

August 1, 2025
Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

August 1, 2025
Ministan Tsaron Kasar Sin Ya Nanata Shan Damarar PLA A Kan Sake Hadewar Kasar

Ministan Tsaron Kasar Sin Ya Nanata Shan Damarar PLA A Kan Sake Hadewar Kasar

August 1, 2025
An Bude Atisayen “Hadin Gwiwa Na Teku Na 2025″ Tsakanin Sin Da Rasha

An Bude Atisayen “Hadin Gwiwa Na Teku Na 2025″ Tsakanin Sin Da Rasha

August 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.