• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kori Tsohon Manajan Banki Bisa Zargin Damfarar Naira Miliyan 122

by Rabi'u Ali Indabawa
7 months ago
in Labarai
0
An Kori Tsohon Manajan Banki Bisa Zargin Damfarar Naira Miliyan 122
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata kotun hukunta manyan laifuka ta Jihar Legas da ke Ikeja ta gurfanar da wani tsohon manajan banki reshen Iju, Abiodun Sanni, a gidan yari bisa zargin damfarar Naira miliyan 122,011,441.

Hukumar Yaki Da Masu Yi Wa Tattalin Arzikin Kasa Zagon Kasa, ta gurfanar da Sanni a gaban kuliya 16 da suka hada da karbar bashi ta hanyar karya, amfani da takardun karya da kuma sata.

  • Bankin Duniya Da IMF Na Kassara Tsarin Ilimin Jami’o’i A Nijeriya – ASUU
  • Karancin Kudin Shiga Ya Jefa ‘Yan Nijeriya Miliyan 14 Cikin Kangin Talauci – Bankin Duniya

Lauyan masu shigar da kara na EFCC, O. Adewunmi, ya shaida wa kotun cewa Sanni ya aikata laifin ne a ranar 24 ga Fabrairu, 2020, a Legas.

Adewunmi ya shaida wa kotun cewa wanda ake kara a lokacin yana manajan bankin Polaris Bank Limited reshen lju, ya samu rance ne a matsayin rancen kudi Naira miliyan 17, kan wani Bamgbose Tayo Taofia da ke kasuwanci da suna da salon Banut Haulage. .

Mai gabatar da kara ya bayyana cewa, an samu kudin ne daga bankin Polaris Bank Limited, ta hanyar karyar cewa bashin na da garantin ne a wani kayyade a asusun ajiya mai lamba 0071572791, kudin da ya kai Naira miliyan 111,540,380.52 mallakin Yinkus Multibiz Bentures da kuma mai ita, daya Misis Olayinka. Hannah Aderibigbe, ta amince a yi amfani da shi a matsayin jingina.

Labarai Masu Nasaba

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Haka kuma an zarge shi da rashin gaskiya da canza wani asusun ajiya na Polaris Bank Limited mai lamba 0071277522 akan kudi Naira miliyan 15, 011,441.00 (Miliyan Goma Sha Biyar, Dubu Sha daya, Dari Hudu da Arba’in da Daya) mallakar Atolagbe Joshua Tinuoye, zuwa amfani da shi.

Sai dai wanda ake tuhumar ya ki amsa laifin da ake tuhumarsa da shi.

Lauyan mai gabatar da kara, ya bukaci kotun da ta ci gaba da tsare wanda ake kara a gidan gyaran hali, har zuwa lokacin da za a fara shari’a.

“Ya Ubangiji, mai gabatar da kara ya yi niyyar gabatar da shaidu 10 game da wannan shari’a kuma muna rokon kotu ta tsare wanda ake kara a gidan yari”, in ji Adewunmi.

Sai dai lauyan da ake kara, Osho Oludoshu, ya shaida wa kotun cewa ya shigar da bukatar neman beli a madadin wanda yake karewa.

A wani takaitaccen hukunci mai shari’a Olubunmi Abike-Fadipe, ta dage ci gaba da sauraron karar tare da bayar da umarnin mika bukatar belin ga kotu kafin ranar da za a fara shari’ar.

“Na dage shari’ar zuwa Match 6 da 19, 2025, kuma na tsare wanda ake kara a gidan gyaran hali. Suna da damar gabatar da takardar neman beli kafin ranar shari’arsa,” in ji alkalin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Banki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotun Birtaniya Ta Daure Wasu ‘Yan Nijeriya 4

Next Post

Dalilin Da Ya Sa Farashin Wake Ba Zai Sauka Ba A Nijeriya -Masana

Related

Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

11 minutes ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

1 hour ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

2 hours ago
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu
Labarai

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

4 hours ago
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara
Labarai

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

5 hours ago
Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai
Labarai

Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

5 hours ago
Next Post
Dalilin Da Ya Sa Farashin Wake Ba Zai Sauka Ba A Nijeriya -Masana

Dalilin Da Ya Sa Farashin Wake Ba Zai Sauka Ba A Nijeriya -Masana

LABARAI MASU NASABA

Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

June 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

June 6, 2025
Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

June 6, 2025
Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89

Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.