ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 21, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

by Leadership Hausa
11 months ago
ADC

Kafin zaɓen shekara ta 2027, jam’iyyar APC da hadakar jam’iyyar ADC na gwagwarmayar neman samun goyon bayan mutanen arewa da kuma wacce ta fi dacewa wajen kare muradunsu.

Shugaban jam’iyyar ADC na wucin gadi kuma tsohon shugaban majalisar dattawa, daɓid Mark, ya bayyana cewa talauci da rashin tsaro da ƙuncin tattalin arziki su ne matsalolin da suke yi wa a arewa katutu.

Shi ma tsohon sakataren gwamnatin tarayya kuma jago a ADC, Babachir Lawal, ya bayyana cewa arewa ta amince da jam’iyyar ADC ta hanyar gamayyar ƙungiyar tuntuɓa kan harkokin siyasa ta ƙasa, a matsayin jam’iyya daya tilo da ta fi kare muradunta tare da alwashin ƙwace mulki a hannun APC a 2027.

ADVERTISEMENT
  • 2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku
  • Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

Mark da Lawal sun bayyana wannan a ranar Asabar a lokacin taron gamayyar ƙungiyar tuntuɓa kan harkokin siyasa ta arewa karo na uku da aka gudanar a Abuja.

da yake mayar da martini kan batun, daraktan Yada Labarai na APC, Bala Ibrahim, ya yi iƙirarin cewa jam’iyyar mai mulki tana da goyon baya a duk faɗin ƙasar nan, ciki har da arewacin Nijeriya, inda ya bayyana cewa muradin ƴan Nijeriya na samun kariya ƙarƙashin gwamnatin Shugaba Bola Tinubu.

LABARAI MASU NASABA

Mutum 1,000 Daga Jam’iyyar ADC Sun Koma PDP A Jihar Katsina

Rashin Tsaro: CUPP Ta Goyi Bayan Kiran Da Aka Yi Wa Tinubu Na Jagoranci Ko Murabus

A yanzu haka dai ratotannin sun tabbatar da cewa APC da ADC suna gogayya wajen neman samun goyon bayan mutanen arewa kafin babban zaɓen 2027 ya ƙariso.

A ranar 1 ga Yuli, manyan ƴan adawa da suka hada da tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar da dan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar LP a 2023, Peter Obi da dan takarar shugaban ƙasa a APC a 2023, Rotimi Amaechi, da tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, sun gabatar da ADC a matsayin hadakar jam’iyyar adawa domin ƙalubalantar Tinubu a 2027.

Shugabannin ADC sun ci gaba da yin ƙoƙari don samun goyon bayan mutanen arewacin Nijeriya da sauran yankuna tun bayan buɗe jam’iyyar.

A taron, Mark ya buƙaci shugabannin arewacin Nijeriya da su daina dabi’ar zargi da kuma amincewa na suna da alhakkin ƙalubalen da yankin ke fuskanta.

Ya ce, “Wannan wata dama ce da kuma girmamawa kasancewa a gabanku yau don magana kan batun halin da muke ciki a yanzu da kuma sauya makomarmu. Ina kira a gare ku mu yi gaggawar samun haɗin kai da ƙarfafa dangantaka a matsayin hanyar magance ƙalubalen da yankinmu ke fuskanta. 

“Arewacin da muka sani ya kasance wata ƙasa ce mai ɗimbin tarihi da albarkatun ma’adinai da ƙasa noma da al’adu masu yawa da kuma ƙarfin tasiri.

“ɗuk da wadannan albarkatu, muna fuskantar ƙalubale masu yawa da suka hada da rashin tsaro da talauci da rikice-rikicen ƙabilanci da addinai da rarrabuwar kai a siyasa da matsalolin zamantakewar da na tattalin arziki. Wadannan ƙalubale ba su faru a dare daya ba kuma ba za su kau ba har sai mun hada kai wajen daukar matakin da ya dace.

“ɗole ne mu yarda da cewa mu ne masu gina matsalolinmu, dole ne mu daina zargin kawunanmu idan muna son samun mafita ɗorewar yankinmu.”

Tsohon shugaban majalisar dattawa ya ƙara bayyana cewa rarrabuwar kawuna ta hana wa arewacin ƙasar nan ci gaba, yayin da halin ko-in-kula da rashin daukan mataki ya ƙara zurfafa rarrabuwar da ta riga ta wanzu.

“ƙalubalen da ke fuskantar arewacin Nijeriya suna da alaƙa da juna. Rashin tsaro yana janyo ficewar masu zuba jari, wanda hakan ke ƙara tsananta talauci. Talauci yana jawo aikata muyagun laifuka. ƙabilanci na rage ƙarfin haɗin kanmu wajen neman kyakkyawan shugabanci. Rugujewar harkokin siyasa na tabbatar da cewa ba za a samu ingantaccen ci gaba a yankinmu. Wannan ba arewar da muka gada ba ne,” in ji ADC.

ɗon dawo da martaban yanki, Mark ya jaddada cewa akwai buƙatar matanen arewa su sake tunani da yin Nazari wajen daukan matakan da suka dace.

Ya kira ga dukkan mutanen arewa su dauki wannan a matsayin babban nauyi na haɓaka haɗin kai wajen inganta yankin maimakon zama a rarrabe.

A nasa ɓangaren, Lawal ya bayyana cewa gamayyyar ƙungiyar tuntuɓa kan harkokin siyasa ta arewa ta amince da ADC a matsayin jam’iyyar da ta iya tunkarar APC a zaɓen 2027.

Tsohon sakataren gwamnatin tarayya ya ce wakilai daga dukkanin jihohin arewa 19 sun cimma yarjejeniya cewa gwamnatin Shugaba Tinubu ba ta wani yuƙuri wajen magance matsalolin yankin. 

Ya ce masu ruwa da tsaki daga arewacin ƙasar nan sun amince su tashi tsaye su yada saƙonsu wajen samn haɗin kan mutane da cimma matsaya kan zaɓe mai zuwa. 

A martaninsa, daraktan yada labarai na APC ya ce jam’iyyar mai mulki ba ta damu da abin da ake kira da suna hadakar jam’iyya ba.

Ibrahim ya bayyana cewa Shugaba Tinubu na jagorantar gwamnati mai cike da samun goyon bayan dukkan mutanen Nijeriya.

Ya ce, “Jam’iyarmu ta APC, tana samun goyon bayan mutanen arewacin Nijeriya da kuma dukkan sauyan yankunan Nijeriya gaba daya, sai dai wadanda ba su gamsu ba da suka kafa jam’iyyar ADC a yanzu.”

Ya bayyana cewa APC ta jajirce wajen sabunta fata ga ƴan Nijeriya kuma yana nuna tabbacin cewa jam’iyyar za ta ƙara samun nasara a 2027.

ADC
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Kotun Ƙoli Za Ta Yanke Hukunci Kan Rikicin PDP Da ADC Yau
Siyasa

Mutum 1,000 Daga Jam’iyyar ADC Sun Koma PDP A Jihar Katsina

June 19, 2026
Tinubu
Siyasa

Rashin Tsaro: CUPP Ta Goyi Bayan Kiran Da Aka Yi Wa Tinubu Na Jagoranci Ko Murabus

June 18, 2026
2027: Tsohon Kakakin Majalisar Kaduna Abdulfatah Ya Zama Ɗan Takarar Gwamnan PRP
Siyasa

2027: Tsohon Kakakin Majalisar Kaduna Abdulfatah Ya Zama Ɗan Takarar Gwamnan PRP

June 18, 2026
Next Post
Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Wasa 23 Da Eric Chelle Ya Gayyata Domin Buga Wasannin Sada Zumunci 

Duk Da Rashin Halartar ‘Super Eagles’ Gasar Kofin Duniya, Nijeriya Ba Ta Rasa Wakilai Ba

June 20, 2026
Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin

Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin

June 20, 2026
Darussan Da Suka Fi Dacewa A Fahimta Daga Alkur’ani A Wannan Zamanin (2)

Hijira: Malaman Musulunci Sun Buƙaci  Musulmi Su Yi Riƙo Da Gaskiya Da Adalci

June 20, 2026
Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire

Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire

June 20, 2026
Nijeriya

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Sin Na Kira Ga Al’ummun Kasa Da Kasa Da Su Himmatu Wajen Tallafawa Ayyukan Jin kai

Sin Na Kira Ga Al’ummun Kasa Da Kasa Da Su Himmatu Wajen Tallafawa Ayyukan Jin kai

June 20, 2026
Sojoji Sun Kashe Mayakan Boko Haram 6, Sun Kama Wasu A Borno

Sojoji Sun Ceto Mutane 22 A Jihar Sakkwato

June 20, 2026
A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki

A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki

June 20, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
IMF

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

June 20, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.