• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yunkurin ACF Na Mara Wa Dan Takarar Arewa Baya A 2027 : Ta Ina Za A Fara?

by Yusuf Shuaibu
9 months ago
in Labarai, Siyasa
0
Yunkurin ACF Na Mara Wa Dan Takarar Arewa Baya A 2027 : Ta Ina Za A Fara?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu jiga-jigan kungiyar tuntuba ta Arewa (ACF) sun yi wani sabon yunkuri na mara baya ga dan takarar shugaban kasa daga arewa a zaben 2027, wanda suke ganin cewa dan yankin arewa ne kadai zai iya kishin magance tarin matsaloli da yankin ke fuskanta a halin yanzu.

Wannan matsayi ya fito ne a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun, Sakataren Yada Labarai na ACF na kasa, Farfesa Tukur Muhammad Baba, kuma ya raba wa manema labarai bayan taron majalisar zartaswa ta kasa da kungiyar ta gudanar a Kaduna.

  • Bayani Kan Zubewar Gashi
  • Zulum Ya Yi Kira Ga Sanatocin Arewa Da Su Ƙi Yarda Da Sabon Tsarin Haraji

Sanarwar ta ce, taron majalisar zartarwa ta ACF, ya yi bitar abubuwan da ke faruwa a arewa da ma kasa baki daya.

“An gudanar da taron majalisar zartarwa ta kasa na kungiyar ACF a hedikwatarta da ke Kaduna a ranar Laraba 20 ga Satumba, 2024. Wakilai a taron sun fito ne daga jihohin arewa da kuma mambobin kungiyar da ke zaune a kasashen waje, wanda shugaban majalisar zartarwa ta kungiyar, Mamman Mike Osuman, ya jagoranta. Taron ya duba ayyukan ACF tun daga taron na Mayun 2024.”

“A jawabinsa na bude taron, shugaban ya yi maraba da mambobin kungiyar tare da nuna gamsuwa da sake farfado da harkokin kungiyar ACF a matsayinta na babbar kungiyar da ke kare muradu, al’adu da zamantakewar al’umma, wadda ke kokarin hada kan al’ummar arewa daban-daban da mabanbantan ra’ayi da manufa daya, tare da hadin kai wajen ganin an cimma nasarar gudanar muradun al’ummar arewa a cikin Nijeriya. Shugaban ya ja kunnen ‘yan kungiyar da su ci gaba da mai da hankali, musamman kan muradun arewa da kuma manufofin ACF, domin akwai abubuwa da yawa da ya kamata a yi kuma lokaci ya kure.

Labarai Masu Nasaba

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

“Shugaban ya umurci sauran shugabannin kungiyar na rassa daban-daban su kasance cikin manufa guda, tare da kawar da bambance-bambancen addini da na kabilanci, amma su yi kokarin tabbatar da dangantaka mai kyau da gwamnonin jihohi.

“Daga wurin taron, an tattauna batun yanayin yadda al’ummar arewa da ma Nijeriya suke fuskar, inda aka mayar da hankali kan tattalin arziki, yanayin da ake ciki, tsaro, kalubalen zamantakewa, zaman lafiya, da ci gaban siyasa.

“Taron ya yi nuni da cewa, al’ummar arewa na ci gaba da fuskantar tabarbarewar al’amura, kasancewar a halin yanzu yankin ya fi samun koma-bayan tattalin arziki idan aka kwatanta da sauran sassan Nijeriya.

“Yankin na fama da matsananciyar rashin wadataccen abinci, kuma matasansa ba su da ilimi da sanin makamar aiki. Yanzu ne lokacin yin tunani. Duk da irin halin da Arewa ke ciki na fuskantar kalubalen tattalin arziki, manufofin gwamnatin tarayya na ci gaba da dagula al’amura, tare da nuna rashin sanin ya kamata dangane da halin da al’ummar arewa ke ciki.

“Kira ga gwamnatin tarayya karkashin jagorancin Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da ta sake duba al’amura da sake tsara alkiblar manufofinta na tattalin arziki ta yadda za su dace da bukatun al’ummar arewa.

“Muna kira da babbar murya ga gwamnonin jihohin arewa da su rungumi tsarin aiwatar da manufofi masu karfi, tare da hadin kai, musamman ta fuskar tsaro, ilimi, koyon sana’o’i, noma, da harkokin kiwon lafiya.

“Rashin wadatar wutar lantarki zai ci gaba da kawo cikas ga kokarin da ake na magance fatara, rashin aikin yi, da rashin ci gaba a yankin. Wadannan dole ne a magance su cikin gaggawa.”

Kungiyar ta ce wannan mataki na da nufin ceto yankin arewa daga gazawar shugabanci da matsalolin da ake fuskanta.

ACF ta nuna goyon bayanta ga kungiyar ‘League of Northern Democrats’ (LND), wata sabuwar kungiya da ta dukufa wajen magance matsalolin yankin arewa, ciki har da rashin aikin yi, ilimi, da tasirin siyasa.

Kawunan dattawan arewa dai ya rabu a zaben 2023, duk da dai ACF da NEF sun bayyana cewa bakin su a hade yake, amma kowa ya nuna cewa ba haka ba ne.

Ta ina kangiyar ACF za ta fara? Sabon abu ne za ta zo da shi ko kuma ta yaya lamarin zai tabbata?

Tun da na farko, akwai kalubalen hadin kai a arewa, saboda yanayin yadda aka farraka kabilu, maimakon kishin arewa, wanda a baya babu maganar kai dan arewa ta kudu ne ko ta tsaki. Amma yanzu da yawan kabilu a arewa idan a ce musu su ‘yan arewa, sai su ce su ba ‘yan arewa ba ne.

Wannan yunkuri abu ne mai kyau kamar yadda wasu yankuna suke yi. Kungiyar Yarbawa an ga yadda take magana da murya daya. Haka nan kungiyar dattawan Ibo suma suna da wannan. Amma yanzu a arewa babu kungiya guda daya tilo, wanda ko a kungiyar dattawan arewa sun rabu kashi buyu, haka kuma kungiyar Fulani ta Meyatt Allah ta rabu kashi-kashi.

Masana suna ganin cewa tana ita za a fara irin wannan yunkurin a yankin arewa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Siyasa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yara 160,000 Ke Rayuwa Da Cutar Ƙanjamau A Nijeriya —NACA

Next Post

ICPC Na Bin Diddigin Ayyukan Mazabu Na Naira Biliyan 21 A Kaduna

Related

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC
Labarai

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

2 hours ago
Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya
Ra'ayi Riga

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

4 hours ago
Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas
Labarai

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

7 hours ago
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa
Labarai

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

8 hours ago
Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP
Manyan Labarai

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

11 hours ago
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru
Manyan Labarai

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

23 hours ago
Next Post
ICPC Na Bin Diddigin Ayyukan Mazabu Na Naira Biliyan 21 A Kaduna

ICPC Na Bin Diddigin Ayyukan Mazabu Na Naira Biliyan 21 A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

August 24, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

August 24, 2025
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

August 24, 2025
An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

August 24, 2025
Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

August 24, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

August 24, 2025
Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

August 24, 2025
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

August 24, 2025
Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

August 24, 2025
Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

August 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.