• English
  • Business News
Tuesday, July 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Nawa Za A Bani Ba Zan Iya Fitowa A Matsayin Kwarto Ko Dan Daudu A Fim Ba -Dan Asabe Olala

by Abubakar Sulaiman
7 months ago
in Nishadi
0
Ko Nawa Za A Bani Ba Zan Iya Fitowa A Matsayin Kwarto Ko Dan Daudu A Fim Ba -Dan Asabe Olala
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da wasu ke daukar harkar fim a matsayin wata hanya na neman kudi kawai, daya daga cikin manyan dattijai a cikin masana’antar Kannywood Alhaji Dan Asabe Garba ko kuma Olala ya ce akwai wasu ayyuka da ba zai iya yi ba ko nawa kuwa za a ba shi.

A lokacin da zan shiga harkar fim, masoya,iyalai da ‘yan uwa sun so su hana ni saboda a nasu tunanin zan iya yin wani abinda zai iya zubar masu da mutuncinsu amma ganin ina matukar sha’awar harkar ya sa dole suka hakura na shiga amma da sharudda biyu, na farko shi ne ba zan taba fitowa a cikin shirin fim a matsayin Dan Daudu ba hakazalika ba zan fito a matsayin Kwarto ba.

  • Na Samu Wata Harkar Da Ta Fi Sana’ar Fim Kawo Kudade -Ali Dawayya
  • Ana Yi Wa ‘Yan Fim Kallon Malamai A Zamanin Baya -Ali Rabi’u Ali

Yanzu haka a kan wannan matsaya ya sa suka barni ina yin wannan harkar, saboda haka ko nawa wani zai bani a kan in karya wannan alkawari da na daukar wa ‘yan uwana da iyalina ba zan karba ba saboda mutunci ya fi komai in ji Dan Asabe Olala wanda ya shafe tsawon shekaru ana damawa da shi a masana’antar Kannywood.

Dangane da kalubalen da masana’antar Kannywood ke fuskanta a halin yanzu, Olala ya ce daga cikin kalubale da ke damun Kannywood akwai rashin jari wanda ya sa an samu karancin yin fina-finai ba kamar a kwanakin  baya da za kaga ayyuka sun yi yawa ba,a wancan lokacin a kan hada karfi mutum biyu ko uku su shirya fim daya saboda za a kai fim kasuwa a sayar kowa a bashi kudinsa.

Amma yanzu saboda yadda aka koma fina-finai masu dogon zango da dama mutane basu da isassun kudaden da za su saka wajen shirya manyan fina-finai da ake shiryawa a yanzu, saboda haka da ace zan samu shugabancin wannan masana’antar zan mayar da hankalina kacokan wajen hada kan mambobin masana’antar ta Kannywood.

Labarai Masu Nasaba

Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

Fim Babbar Hanya Ce Ta Nishaɗantar Da Al’umma -D Malam Dan Bola (2)

Sannan kuma in tafi wajen samo masu hannu da shuni domin su zo su zuba hannayen jarinsu a wannan masana’antar, zaka ga da dama mutane na sha’war zuba hannayen jarinsu a wannan masana’antar amma ba su san yadda za su yi ba ko kuma hanyoyin da za su bi wajen ganin ba su yi asarar kudadensu da su ka zuba a harkar ba.

Daga karshe Alhaji Dan Asabe ya shawarci matasa mata da maza da ke da sha’awar shigowa wannan masana’antar domin su fara harkar fim a kan duk wanda zai shigo ya tabbatar da cewar zai iya hakuri har zuwa lokacin da Allah zai nufi ya samu daukaka, domin kuwa a dare daya ba zai samu abin da yake so ba dole sai ya jajirce ya kuma yi hakuri kamar yadda wadanda yake gani sun samu daukaka suka yi kafin shima ya zama wani abu a Kannywood.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FimHausaHausa Fim
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Da Faransa Sun Gudanar Da Taron Tattaunawa Bisa Matsayin Koli Karo Na 26 

Next Post

Yadda Wasan Manchester Derby Ya Kaya A Etihad 

Related

Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda
Nishadi

Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

2 days ago
Fim Babbar Hanya Ce Ta Nishaɗantar Da Al’umma -D Malam Dan Bola (2)
Nishadi

Fim Babbar Hanya Ce Ta Nishaɗantar Da Al’umma -D Malam Dan Bola (2)

1 week ago
Rashin Abinci Na A Waka Ya Sa Na Daina Yi -T Y Shaba
Nishadi

Rashin Abinci Na A Waka Ya Sa Na Daina Yi -T Y Shaba

3 weeks ago
Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu
Nishadi

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

1 month ago
Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 
Nishadi

Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

1 month ago
Hukuma Ta Dakatar Da Haska Fina-Finai 22 Har Sai Baba Tagani
Nishadi

Hukuma Ta Dakatar Da Haska Fina-Finai 22 Har Sai Baba Tagani

1 month ago
Next Post
Yadda Wasan Manchester Derby Ya Kaya A Etihad 

Yadda Wasan Manchester Derby Ya Kaya A Etihad 

LABARAI MASU NASABA

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

July 1, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

July 1, 2025
An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

July 1, 2025
Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

July 1, 2025
Kayan Aro Baya Rufe Katara

Kayan Aro Baya Rufe Katara

July 1, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Askarawan Zamfara Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga, Kacalla Ɗanbokolo Ubangidan Turji

July 1, 2025
Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

July 1, 2025
Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

July 1, 2025
Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

July 1, 2025
An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

July 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.