• English
  • Business News
Tuesday, October 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Ɓangaren Bafarawa Kan Rikicin Shugabannin PDP A Sakkwato

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
9 months ago
Kotu

Babbar kotun Jihar Sakkwato, ta yi watsi da ƙarar da ɓangaren tsohon gwamnan jihar, Attahiru Bafarawa, suka shigar, inda suke ƙalubalantar sahihancin zaɓen shugabannin jam’iyyar PDP na jihar.

A hukuncin da ya yanke, mai shari’a Kabiru Ahmad ya bayyana cewa zaɓen shugabannin jam’iyya lamari ne da ya shafi cikin gida na jam’iyyar, don haka waɗanda suka shigar da ƙarar ba su da hurumin yin hakan.

  • Hare-haren ‘Yan Bindiga Sun Ragu A Watan Disamban 2024, Amma Har Yanzu Ana Fuskantar Barazana – Rahoto
  • Mahalarta Ɗaurin Aure 19 Daga Kano Sun Rasu A Hatsarin Mota A Filato

Ya ce kotu ba ta da zaɓi face ta kori ƙarar.

Rikici ya kunno kai a PDP tun bayan zaɓen 2023, musamman a ƙarƙashin jagorancin tsohon gwamna Aminu Waziri Tambuwal.

Rikicin ya ƙara tsananta a lokacin zaɓen shugabannin mazaɓu na jam’iyyar a 2024, inda ɓangaren da ke goyon bayan Attahiru Bafarawa suka yi zargin rashin adalci.

LABARAI MASU NASABA

Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 

Kotu A Kano Ta Tsare Wani Mai Gidan Marayu Bisa Zargin Satar Yara Da Safararsu Zuwa Delta

Ɓangaren Bafarawa sun kai ƙarar gaban kotu, suna neman a soke zaɓen shugabannin mazaɓu, suna zargin cewa an hana wasu ’ya’yan jam’iyyar damar sayen fom ɗin tsayawa takara domin a sharewa wasu hanya.

Lauyansu, Ibrahim Abdullah, ya ce hakan ya saɓa wa dokar zaɓe ta 2022 da kuma kundin tsarin mulkin ƙasa.

Sai dai, ɓangaren PDP da Bello Goronyo ke jagoranta sun musanta zargin.

Lauyan jam’iyyar, A.Y. Abubakar, ya shaida wa kotu cewa waɗanda suka kai ƙarar ba su da rajistar jam’iyyar, kuma lamuran da suka shafi zaɓen shugabannin jam’iyya ya kamata a warware su a cikin gida, ba gaban kotu ba.

Bayan sauraron ɓangarorin biyu, kotu ta yanke hukuncin korar ƙarar, tana mai cewa ba ta da hurumin shiga cikin rikicin cikin gida na jam’iyyar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 
Labarai

Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 

October 14, 2025
Kotu
Manyan Labarai

Kotu A Kano Ta Tsare Wani Mai Gidan Marayu Bisa Zargin Satar Yara Da Safararsu Zuwa Delta

October 14, 2025
Asuu
Labarai

An Janye Wajibcin Samun Kiredit A Darasin Lissafi Ga Ɗaliban Fannin Zamantakewa Don Shiga Manyan Makarantu 

October 14, 2025
Next Post
Xi Ya Zanta Da Shugaban Majalisar Tarayyar Turai Ta Tarho

Xi Ya Zanta Da Shugaban Majalisar Tarayyar Turai Ta Tarho

LABARAI MASU NASABA

Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

October 14, 2025
Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 

Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 

October 14, 2025
Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 

Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 

October 14, 2025
Kotu

Kotu A Kano Ta Tsare Wani Mai Gidan Marayu Bisa Zargin Satar Yara Da Safararsu Zuwa Delta

October 14, 2025
Kowacce Mace Tauraruwa Ce A Kasar Sin

Kowacce Mace Tauraruwa Ce A Kasar Sin

October 14, 2025
Shawarwarin Sin Sun Bude Sabuwar Hanyar Bunkasa Ci Gaban Mata A Duniya

Shawarwarin Sin Sun Bude Sabuwar Hanyar Bunkasa Ci Gaban Mata A Duniya

October 14, 2025
Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Benin A Uyo

Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Benin A Uyo

October 14, 2025
Asuu

An Janye Wajibcin Samun Kiredit A Darasin Lissafi Ga Ɗaliban Fannin Zamantakewa Don Shiga Manyan Makarantu 

October 14, 2025
Al’ummun Kasashe Daban-Daban Sun Yabawa Shawarwarin Sin Dake Taimakawa Wajen Dunkulewa Don Hanzarta Ci Gaban Mata

Al’ummun Kasashe Daban-Daban Sun Yabawa Shawarwarin Sin Dake Taimakawa Wajen Dunkulewa Don Hanzarta Ci Gaban Mata

October 14, 2025
Majalisar Wakilai Ta Buƙaci Hukumomin Tsaro Su Kai Agajin Gaggawa A Sakkwato

Majalisar Wakilai Ta Buƙaci Hukumomin Tsaro Su Kai Agajin Gaggawa A Sakkwato

October 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.