• English
  • Business News
Thursday, May 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

RIGATA 2025: Mun Shirya Tsaf Don Baje Kolin Al’adun Gargajiya Kamar Yadda Aka Saba

by Abdullahi Yelwa
4 months ago
in Rahotonni
0
RIGATA 2025: Mun Shirya Tsaf Don Baje Kolin Al’adun Gargajiya Kamar Yadda Aka Saba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Alummar Masarautar Yauri da ke a kudancin Jihar Kebbi, sun shirya tsaf, domin gudanar da bikin gargajiya na Rigata.

An shafe sama da shekaru 200 ana gudanar da wannan bikin gargajiyar wanda kuma ba a ciki ganin irinsa, a kasar nan ba, saboda ana gudanar da bikin ne, kan tudu da kuma gudanar da wasanni, a kan Kogin Neja.

  • Sin Ta Samar Da Yuan Biliyan 6.66 Don Gudanar Da Ayyukan Farfado Da Kauyuka Dake Yankunan Kananan Kabilu
  • Kar Ku Tayar Da Hankalinku Kan Cutar Tsuntsaye – Ma’aikatar Lafiya Ta Kano

Kazalika, ana gudanar kade-kade da raye-raye, wasanni a kan kogi da kuma nuna alkarcin fannin aikin noma da Allah ya wadaci Masarautar da su.

Bkin na da nasaba da hudda a tsakanin ‘yan Adam da kuma dabbibin ruwa, kamar Dorinar ruwa, Kada wadanda suke ke kai wa bil Adama hari, tare da janyo mutuwar su.

Domin a dakile wannan barazanar hakan ke sanya wa a duk shekara,  jaruman Gungu, suka shiga cikin Kwale-Kwale dauke da makamai sun yi farautar irin wadannan mugayen dabbobin ruwan.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

Suna kuma yin hakan ne, domin su samar da tsaro a kan Kogunna da tabbatar da zirga-zirga a cikin sauki da kuma kara habaka sauran hada-hadar kawuanci a Kogunan.

Bayan zuwa Turwan mallaka a karni na 19, an haramta farautar Dorinar ruwa, sai dai, daga baya, an ci gaba da yi a  bikin na Rigata, domin a nuna irin karfin da Masarautar take da shi, musamman a lokutan bukukuwan aure.

Kai ziyarar da marigayi Sardaunan Sokoto kuma Firimiyan Arewa Sir Ahmadu Bello, a yankin na Yauri, hakan ya sake farfado da bikin na Rigata, wanda lokacin ziyararsa, aka gudanar da wasanni da kuma baje kolin amfanin gona, domin a karrama shi.

Bisa jajircwar Mai Martaba Sarkin Yauri Dakta Mohammad Zayyanu Abdullahi, CON, da kuma namjin kokarin gwamnan jihar, an sake farfado da bikin karo na 42.

Mayar da hankali da Dakta Nasir Idris da kuma, Kauran Gwandu, Gamjin Yauri, ya taimaka matuka wajen farfado da martabar bikin.

Kazalila, tsarin da Gwamna Idris ya samar na daga darajar yawon bude Ido a jihar, hakan ya kara janyo ra’ayin bunkasar bukukuwan gargajiya a jihar.

Misali, manya bukukuwan gargajiya kamarsu, bikin kamun Kifi na kasa da kasa na Argungu da ake gudanarwa a garin Argungu,bikin gargajiya na the Uhola.

Bikin gargajiya na Zuru da ake yi a yankin Geandu, ya taimaka wajen daga darajar yawon bude Ido na jihar  Kebbi a Idon duniya.

Duba da yadda ake gudanar da manyan bukukuwan gargajiya a kasar, sai dai, akwai wasu manyan kalubale nan a ci gaba da gudanar da bukuwan da kuma karancin kudi, musamman domin a ci gaba da gudanar da bukukuwan.

Bukukuwa da dama, sun bace bat, saboda rashin kudin ci gaba da gudanar da su, wasu ma, tun daga matakin farkon fara gudanar da su.

Idan har ana son gudanar da bukukuwan gargajiya su ci gaba da dorewa, dole ne, alumma su bayar da na su goyon bayan, musamman wajen samar da kudade.

Bikin na  Rigata, na daga cikin manyan bukuwan da ke a kasar ana kuma gudanar da bikin ne, a duk shekara a cikin watan Fabirairun.

Ana fara gudanar da bikin ne, ta hanyar baje kolin amfanin gona, sai kuma nuna al’adun gargajiya da kade-kade da kuma raye-raye, tare da yin gasar kokawar gargajiya.

A bikin ana gudanar da gasar wasa da Kwale-Kwale a kan Kogi, inda kuma a bikin ya hada da, ‘yan tawagar kai Amarya tare da yi mata rakiya da kade-kade a  cikin Jirgin Kwale-Kwalen da aka yi masa ado

A baya, ana yi wa Amaryar rakia ne, zuwa gidan mijinsu a cikin Kwale-Kwale, musamman a yankunan da ake da Rafuka.

A 2023, an karamma Gwamnan jihar Dakta Nasir Idris a wajen bikin na bara da wakar Gambara, wacce ita ce ta farko, da aka fara gabatarwa a lokacin bikin.

A yayin da ake shirye-shiryen gudanar da bkin na bana, ‘yan Nijeriya na ci gaba da sa ido, domin su ga yadda bikin na zai gabatar da wasu sabbin dabaru, musamman a bangaren kade-kade.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: RahotoRigata
ShareTweetSendShare
Previous Post

Janar Murtala Mohammed: Ba Rabo Da Gwani Ba…

Next Post

Ƴansanda Sun Gano Motoci 2 Da Aka Sace A Kano

Related

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi
Rahotonni

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

3 weeks ago
Janar Tiani Ya Fara Sabon Mulkin Shekaru Biyar A Nijar
Rahotonni

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

4 weeks ago
An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya
Rahotonni

An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya

4 weeks ago
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Rahotonni

Amurka Ta Sayi Kayayyakin Nijeriya Na Dala Miliyan 643 A Wata 2 – Rahoto

4 weeks ago
Gwamnoni 20 Na Fuskantar Matsin Lambar NULGE Kan Rashin Aiwatar Da Mafi Karanci Albashi
Rahotonni

Gwamnoni 20 Na Fuskantar Matsin Lambar NULGE Kan Rashin Aiwatar Da Mafi Karanci Albashi

4 weeks ago
Tinubu
Manyan Labarai

Yadda Tinubu Ya Shirya Wa Kansa Mafitar Siyasa Kafin Zaben 2027

2 months ago
Next Post
Ƴansanda Sun Gano Motoci 2 Da Aka Sace A Kano

Ƴansanda Sun Gano Motoci 2 Da Aka Sace A Kano

LABARAI MASU NASABA

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

May 8, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

May 8, 2025
An Yi Taron Musayar Al’adu Da Cudanyar Jama’a Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Nasarar Yakin Da Sinawa Suka Yi Kan Zaluncin Japan Da Yakin Ceton Kasa Na Tsohuwar Tarayyar Soviet

An Yi Taron Musayar Al’adu Da Cudanyar Jama’a Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Nasarar Yakin Da Sinawa Suka Yi Kan Zaluncin Japan Da Yakin Ceton Kasa Na Tsohuwar Tarayyar Soviet

May 8, 2025
Zamalek Ta Sallami Tsohon Kocin Super Eagles, Peseiro

Zamalek Ta Sallami Tsohon Kocin Super Eagles, Peseiro

May 8, 2025
Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Halartar Taron Sauyin Yanayi A Dubai

Tinubu Ya Kai Ziyarar Aiki Jihar Anambra

May 8, 2025
Almundahana: LP Ta Nada Sanata Ireti Kingibe Domin Binciken Tsohon Shugaban Jam’iyyar

Almundahana: LP Ta Nada Sanata Ireti Kingibe Domin Binciken Tsohon Shugaban Jam’iyyar

May 8, 2025
Zamfara Ta Haɗa Gwiwa Da Oracle A Landan Don Bunƙasa Fasahar Matasa A Jiharta 

Zamfara Ta Haɗa Gwiwa Da Oracle A Landan Don Bunƙasa Fasahar Matasa A Jiharta 

May 8, 2025
Ko Kun San Dalilin EFCC Na Kama Gudaji Kazaure

Ko Kun San Dalilin EFCC Na Kama Gudaji Kazaure

May 8, 2025
Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Taron Musayar Al’adu Tsakanin Sin Da Rasha 

Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Taron Musayar Al’adu Tsakanin Sin Da Rasha 

May 8, 2025
Isra’ila Ta Yi Barazanar Kai Hare-Hare Kan Iran Kamar Hamas Da Hezbollah

Isra’ila Ta Yi Barazanar Kai Hare-Hare Kan Iran Kamar Hamas Da Hezbollah

May 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.