• English
  • Business News
Monday, July 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Sudan: Gwamna Lawal Ya Bayar Da Aiki Kai Tsaye Ga Ɗaliban Zamfara 16 Da Suka Kammala Karatun Aikin Jinya

by Sulaiman
5 months ago
in Labarai
0
Rikicin Sudan: Gwamna Lawal Ya Bayar Da Aiki Kai Tsaye Ga Ɗaliban Zamfara 16 Da Suka Kammala Karatun Aikin Jinya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya bai wa daliban jihar su 16 da suka kammala karatun aikin jinya a jami’ar Sudan ta ƙasa da ƙasa nan take.

A ranar Alhamis ne Gwamna Lawal ya miƙa wa ɗaliban Jihar Zamfara da suka kammala karatun aikin jinya takardar shaidarsu daga jami’ar Sudan a gidan gwamnati da ke Gusau.

  • Gwamnati Ta Kara Yawan Kudaden Shiga Da Ake Bukatar FIRS Ta Tara A 2025
  • Bullar Cutar Da Ke Lalata Citta Ta Sa Farashinta Ya Sake Karuwa A Karo Na Shida

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar, Sulaiman Bala Idris ya fitar, ta bayyana cewa an kwashe ɗalibai 66 da gwamnatin jihar Zamfara ta ɗauki nauyin karatunsu daga ƙasar Sudan a shekarar 2023 sakamakon rikicin da ake fama da shi a ƙasar.

Sanarwar ta ƙara da cewa, 16 daga cikin 66 da aka kora ɗalibai ne na aikin jinya waɗanda suka kasa yin jarrabawar ƙarshe kafin a fara yaƙin.

“A watan Satumbar 2023, Gwamna Dauda Lawal ya ɗauki matakin jin ƙai don taimakawa ɗaliban Zamfara 66 da aka kwashe daga Sudan.

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

“A bisa umarnin gwamna, kwamishinan ilimi na jihar Zamfara ya haɗa hannu da mahukuntan jami’ar Sudan domin gudanar da jarrabawar ɗalibai 16 na shekarar ƙarshe, wanda aka gudanar a Nijeriya.

“Jami’ar ƙasa da ƙasa ta Sudan ta aike da takardar shaidar kammala jarrabawar ɗaliban jami’ar jinya 16 da gwamna ya ba su.

A yayin gabatar da takardar shaidar, Gwamna Lawal ya ƙara wa ɗaliban da suka kammala karatun kwarin gwiwar zama jakadu nagari a Zamfara da kuma shiga ayyukan gwamnati na ceto jihar.

“Gwamnatina ta kafa dokar ta-baci a fannin ilimi, inda ta magance matsalolin da ke addabar jihar Zamfara. A halin yanzu muna samun ci gaba mai ma’ana kuma za mu zage damtse wajen saka jari mai yawa a cikin ilimi yayin da yake zama tushen ingantacciyar al’umma.

“Kwamishinan ya bayyana abubuwan da muka fuskanta kafin kammala karatun ku. Muna alfahari da ku.

“Muna ginawa da gyara asibitoci a duk faɗin jihar, amma ba a nan gizo ke saƙa ba. Ba zai yiwu a yi gine-gine ba tare da aikin da ake buƙata ba, don haka kun zo a lokacin da ya dace.

“Kun bi wannan fanni mai ɗimbin fa’ida na aikin jinya, kuma a sakamakon haka, za a ba ku aiki kai tsaye daga gwamnatin jihar Zamfara. Shugaban ma’aikata zai tabbatar da samun aikin ku a gwamnatin Zamfara a hukumance. Ina taya ku murna.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Bullar Cutar Da Ke Lalata Citta Ta Sa Farashinta Ya Sake Karuwa A Karo Na Shida

Next Post

Hanyoyi Biyar Da Gwamnatin Tarayya Ta Samar Don Dakile Karancin Abinci A 2025

Related

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato
Da ɗumi-ɗuminsa

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

9 hours ago
Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a
Labarai

Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

11 hours ago
Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson
Labarai

Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

12 hours ago
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Manyan Labarai

Ranar Talata Mai Zuwa Zan Koma Zauren Majalisar Dattawa – Sanata Natasha

14 hours ago
Za A Fara Sufurin Ma’aikata Da Ɗaliban Kaduna Kyauta A Bas
Labarai

Za A Fara Sufurin Ma’aikata Da Ɗaliban Kaduna Kyauta A Bas

18 hours ago
Mutane 8 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsari A Hanyar Lagos
Labarai

Mutane 8 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsari A Hanyar Lagos

19 hours ago
Next Post
Hanyoyi Biyar Da Gwamnatin Tarayya Ta Samar Don Dakile Karancin Abinci A 2025

Hanyoyi Biyar Da Gwamnatin Tarayya Ta Samar Don Dakile Karancin Abinci A 2025

LABARAI MASU NASABA

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

July 6, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

July 6, 2025
Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

July 6, 2025
Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

July 6, 2025
Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

July 6, 2025
Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

July 6, 2025
Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

July 6, 2025
Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

July 6, 2025
Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin

Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin

July 6, 2025
Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum

Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum

July 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.