ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Sudan: Gwamna Lawal Ya Bayar Da Aiki Kai Tsaye Ga Ɗaliban Zamfara 16 Da Suka Kammala Karatun Aikin Jinya

by Sulaiman
1 year ago
Sudan

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya bai wa daliban jihar su 16 da suka kammala karatun aikin jinya a jami’ar Sudan ta ƙasa da ƙasa nan take.

A ranar Alhamis ne Gwamna Lawal ya miƙa wa ɗaliban Jihar Zamfara da suka kammala karatun aikin jinya takardar shaidarsu daga jami’ar Sudan a gidan gwamnati da ke Gusau.

  • Gwamnati Ta Kara Yawan Kudaden Shiga Da Ake Bukatar FIRS Ta Tara A 2025
  • Bullar Cutar Da Ke Lalata Citta Ta Sa Farashinta Ya Sake Karuwa A Karo Na Shida

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar, Sulaiman Bala Idris ya fitar, ta bayyana cewa an kwashe ɗalibai 66 da gwamnatin jihar Zamfara ta ɗauki nauyin karatunsu daga ƙasar Sudan a shekarar 2023 sakamakon rikicin da ake fama da shi a ƙasar.

ADVERTISEMENT

Sanarwar ta ƙara da cewa, 16 daga cikin 66 da aka kora ɗalibai ne na aikin jinya waɗanda suka kasa yin jarrabawar ƙarshe kafin a fara yaƙin.

“A watan Satumbar 2023, Gwamna Dauda Lawal ya ɗauki matakin jin ƙai don taimakawa ɗaliban Zamfara 66 da aka kwashe daga Sudan.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

“A bisa umarnin gwamna, kwamishinan ilimi na jihar Zamfara ya haɗa hannu da mahukuntan jami’ar Sudan domin gudanar da jarrabawar ɗalibai 16 na shekarar ƙarshe, wanda aka gudanar a Nijeriya.

“Jami’ar ƙasa da ƙasa ta Sudan ta aike da takardar shaidar kammala jarrabawar ɗaliban jami’ar jinya 16 da gwamna ya ba su.

A yayin gabatar da takardar shaidar, Gwamna Lawal ya ƙara wa ɗaliban da suka kammala karatun kwarin gwiwar zama jakadu nagari a Zamfara da kuma shiga ayyukan gwamnati na ceto jihar.

“Gwamnatina ta kafa dokar ta-baci a fannin ilimi, inda ta magance matsalolin da ke addabar jihar Zamfara. A halin yanzu muna samun ci gaba mai ma’ana kuma za mu zage damtse wajen saka jari mai yawa a cikin ilimi yayin da yake zama tushen ingantacciyar al’umma.

“Kwamishinan ya bayyana abubuwan da muka fuskanta kafin kammala karatun ku. Muna alfahari da ku.

“Muna ginawa da gyara asibitoci a duk faɗin jihar, amma ba a nan gizo ke saƙa ba. Ba zai yiwu a yi gine-gine ba tare da aikin da ake buƙata ba, don haka kun zo a lokacin da ya dace.

“Kun bi wannan fanni mai ɗimbin fa’ida na aikin jinya, kuma a sakamakon haka, za a ba ku aiki kai tsaye daga gwamnatin jihar Zamfara. Shugaban ma’aikata zai tabbatar da samun aikin ku a gwamnatin Zamfara a hukumance. Ina taya ku murna.”

Sudan
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Hanyoyi Biyar Da Gwamnatin Tarayya Ta Samar Don Dakile Karancin Abinci A 2025

Hanyoyi Biyar Da Gwamnatin Tarayya Ta Samar Don Dakile Karancin Abinci A 2025

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.