• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nasarori Da Matsalolin Da NAHCON Ke Samu Wajen Gudanar Da Aikin Hajji

by Musa Muhammad Awwal
3 years ago
in Labarai
0
Nasarori Da Matsalolin Da NAHCON Ke Samu Wajen Gudanar Da Aikin Hajji
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kamar yadda aka sani ne, NAHCON ce ke da alhakin shiryawa tare da gudanar da ayyukan da suka shafi aikin hajji a kasar nan, wanda kuma ita ce ke da alhakin ganin aikin ya gudana ba tare da wata tangarda ba.

Kamar kowace shekara, a bana ma Hukumar ta yi wannan aiki, inda kuma aka samu nasarori masu yawan gaske. Haka kuma, babu yadda za a yi a ce an yi wannan aiki ba tare wata matsala ba.

  • Shugaba Buhari Zai Kawo Karshen Rashin Tsaro A Nijeriya -Buratai
  • Ziyarar Babbar jami’ar Lithuania A Taiwan Shirme Ne

Game da korafin da wasu ke yi na cewa an bar wasu maniyyata a kasa ba su samu tafiya aikin hajjin ba, wannan ba abin korafi ba ne domin Hukumar ta sha bayyana cewa ba duk wanda ya biya kudinsa ne zai samu tafiya ba, don haka ne ma ake fada ma jama’a don su zama cikin shiri.

Saboda haka ga duk mai bibiyar aikin Hajji a duk shekara, sam wannan ba abu ne da ya kamata ya zama abin korafi ba, musamman bisa la’akari da yadda ita kanta Hukumar kasar Sadiyya ta ke rage yawan maniyyatan a duk shekara.

Wani abu mai daure kai kuma shi ne yadda ake samun korafi daga wasu ma’aikatan Hukumar wadanda ba su samu damar zuwa kasar mai tsarki don gudanar ayyukan da aka saba ba, alhali a bayyana ya ke, cewa ba duk ma’aikatan ne za a dade a tafi ba, dole akwai wadanda za a bari a ofis don wasu ayyukan.

Labarai Masu Nasaba

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Bugu da kari, duk wani ma’aikacin da bai samu nasarar tafiya aikin hajjin ba, to akwai wani dan ihsani da ake yi masu a zaman da suke yi a kasar nan.

Amma sai ya zama duk da irin kyakkyawan tsarin da ake da shi wajen zabar ma’aikatan da za su tafi aikin hajjin, abin takaci, sai ya zama wasu suna fusata, har suna shiga kafafen yada labarai sun yin wadansu zarge-zarge marasa tushe.

Haka kuma, rikici ko rashin jituwar da kan faru tsakanin Hukumomin kula da jin dadin Alhazai na jihohi na daga cikin abubuwan da kan kawo tsaiko a harkar jigilar maniyyatan.

Wani babban misali, shi ne irin wanda aka samu tsakanin jihar Kano da kamfanin jirage na Azaman air, da kuma tsakanin jihar Kanon dai da adashen gata, alhali ita NAHCON ta riga ta yi kyakkyawan shiri a kan haka, wanda hakan ya kawo matsaloli.

Saboda haka ga duk wanda ya san irin namijin kokarin da NAHCON ke yi wajen ganin an samu aikin hajji mai cike da nasara, to ba zai damu da wasu kananan maganganu da wasu masu son zuciya ke yi ba.

Ina ganin bisa kyawawan tsare-tsaren da hukumar nan ke yi a duk shekara, to lallai ta cancanci jinjina ne ta musamman, musamman a ‘yan shekarun nan da suka gabata, wanda hakan ya sa suke samun lambar yabo bisa hukumar da ta yi fice wajen iya gabatar da tsari a aikin hajjin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Aikin Hajjin BanaAlhazaiCi GabaJirageMahajjataNAHCONSaudiyya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kungiyar Kawance Ta Sin Da Niger Na Goyon Bayan Manufar Sin Daya Tak

Next Post

“Korar Fulani A Edo: Ina Ake So Wadanda Aka Haifa A Jihar Shekara 50 Su Koma?”

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

6 hours ago
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

7 hours ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

8 hours ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

13 hours ago
NAHCON
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

13 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

14 hours ago
Next Post
“Korar Fulani A Edo: Ina Ake So Wadanda Aka Haifa A Jihar Shekara 50 Su Koma?”

“Korar Fulani A Edo: Ina Ake So Wadanda Aka Haifa A Jihar Shekara 50 Su Koma?”

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.