• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Uba Sani Da El-Rufa’i Ya Dauki Sabon Salo

by Rabi'u Ali Indabawa
3 months ago
in Siyasa
0
Rikicin Uba Sani Da El-Rufa’i Ya Dauki Sabon Salo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rikicin da ake tsakanin tsohon gwamnan Jihar Kaduna da gwamna mai ci Uba Sani na ci gaba da daukar sabon salo, inda dukkaninsu ke kai wa juna hare-hare cikin kalamai.

Gwamna Sani a wata hira da ya yi a gidan talabijin na kasa ranar Litinin ya yi kakkausan suka ga abin da ya kira gamayyar ‘yan siyasa da suka taru kwanan nan don sukar gwamnatin shugaba Bola Ahmed Tinubu.

  • ‘Yan Bindiga Sun Harbe Mutum 2, Sun Yi Garkuwa Da Wasu 5 A Kaduna.
  • Zanga-zanga: Ku Kawo Ƙarshen Rashin Wutar Lantarki Da Ta Addabi Jihohi- Gwamnatin Kaduna 

A cikin hirar, gwamnan ya zarge su da adawa da gwamnati don neman mulki kawai maimakon samar da ingantattun hanyoyin magance kalubalen da ke addabar Nijeriya.

Gwamnan ya bayyana cewa babu daya daga cikin ‘ya’yan kungiyar da zai iya adawa da manufofin dimokuradiyyar Tinubu, yana mai jaddada cewa shugaban ya yi gwagwarmaya kuma ya tsaya tsayin daka wajen tabbatar da dimokradiyya.

Idan dai ba a manta ba a makon da ya gabata ne Tsohon Mataimakin Shugaban Kasa Atiku Abubakar, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour a 2023, Peter Obi, tsohon gwamnan Jihar Rivers, Rotimi Amaechi, tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, da tsohon gwamnan Jihar Ekiti, Kayode Fayemi, na cikin wasu manyan ‘yan siyasa da suka hallara a wani taro a Abuja, inda suka caccaki gwamnatin Shugaba Tinubu da jam’iyyar APC mai mulki.

Labarai Masu Nasaba

Dalilin Gwamnatin Kano Na Haramta Shirye-shiryen Siyasa Kai Tsaye

Gwamna Fintiri Ba Zai Bar PDP Ba – Humwashi

Gwamna Sani ya bayyana zargin da kungiyar ta yi a matsayin maras tushe, yana mai jaddada cewa “Mafi yawan ‘yan siyasar da ke irin wadannan kalamai na iya zama suna magana da kansu ne kawai,” in ji shi. “Mun kasance a cikin jam’iyya daya a wani lokaci, kuma dole ne in ce na yi mamakin abin da suka yi.”

Ya kara da cewa kawancen ba shi da wata hujjoji ta gaskiya kan ikirarin nasu.

“Fito da zarge-zarge ba tare da hujja ba, wani yunkuri ne kawai na kawar da hankulan ‘yan Nijeriya,” in ji gwamnan.

“Yawancin wadannan ‘yan siyasa sun rike mukamai a gwamnati kasa da shekaru biyu da suka gabata. Me suka yi a lokacin da suke kan mulki?”

Ya nuna shakku kan sahihancinsu, yana mai nuni da cewa yakinsu sun yi ne kawai a lokacin suna kan mulki.

“Yan Najeriya suna fa fahimta, kuma sun riga sun san wadannan ’yan siyasa ba wai suna fada da Tinubu ba ne saboda sun fi shi sanin abin da ya fi dacewa da su, a’a sun samu dama a baya amma me suka yi?

Gwamna Sani ya kara da cewa a kwanakin baya wasu ‘yan siyasa sun yaba wa Shugaba Tinubu amma sun canja ra’ayinsu bayan barin gwamnati.

“Mafi yawansu suna zaune a teburi daya da mu, suna yakar Tinubu saboda mun yi imanin cewa shi ne mutumin da ya fi dacewa ya ciyar da kasar nan gaba,” in ji shi. “Mene ne shaidar dimokuradiyya, idan zan iya tambaya? Me suka yi domin ciyar da dimokuradiyya gaba a Nijeriya?” Ya tambaya.

A martanin da El-Rufai ya mayar a shafinsa na D, ya caccaki gwamnan, yana mai cewa, “Mutanen Jihar Kaduna za su yi hukunci.”

El-Rufai, a cikin shafinsa na D mai taken “Kaduna Update,” ya ce gwamnan yana “borin kunya ne da rudani” a kowace rana.

“Ina mamakin dalili, ko da yake na tabbatar da cewa Gwamnatin Tarayya ‘ramawa’ kura aniyarta, ya bai wa Kaduna tallafin da ya haura Naira biliyan 150, a cikin watanni 18 da suka gabata, yanzu ya bayyana komai.”

“Ta kowane hali suke kare Asiwaju don samun kudi bisa sharadi. Asiwaju ya amfana da ku. Al’ummar Jihar Kaduna za su yi hukunci a daidai lokacin da ya dace, kamar yadda ya rubuta.

A wani labarin kuma, El-Rufai ya ruwaito cewa, tsohon firaministan kasar Birtaniya Tony Blair na cewa a wani lokaci da ya gabata: “ Cikin kasashe masu tasowa, inda mutane ke gwagwarmayar sanya abin da za su sa a bakinsu, zuwa makaranta, samun ilimin kiwon lafiya na yau da kullum, samar da rayuwa ba sana’a ba, (ayyukan zamantakewa) bayarwa na iya zama bambanci tsakanin rayuwa da mutuwa; ko akalla bambanci tsakanin rayuwa mai cike da bege da wacce ta sava da hakan.

“Su (‘yan kasa) suna son a magance matsalolin da ke shafar rayuwarsu ko a rage su. Suna son ingantacciyar rayuwa, ingantaccen kiwon lafiya, ilimi da tsaro.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kaduna
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wasu Ruwayoyi Game Da Yafiyar Manzon Allah (SAW)

Next Post

Gwamnatin Tarayya Ta Amince Da Kashe Naira Tiriliyan 4.2 Don Aikin Manyan Hanyoyi

Related

Dalilin Gwamnatin Kano Na Haramta Shirye-shiryen Siyasa Kai Tsaye
Siyasa

Dalilin Gwamnatin Kano Na Haramta Shirye-shiryen Siyasa Kai Tsaye

1 day ago
Gwamna Fintiri Ba Zai Bar PDP Ba – Humwashi
Siyasa

Gwamna Fintiri Ba Zai Bar PDP Ba – Humwashi

4 days ago
Gwamna Abba Kabir Ya Mayar Wa Da Bappa Bichi Martani
Siyasa

Gwamna Abba Kabir Ya Mayar Wa Da Bappa Bichi Martani

5 days ago
Atiku Ne Rikitacce Ba Tinubu Ba
Labarai

Atiku Ne Rikitacce Ba Tinubu Ba

1 week ago
Mataimakin Gwamnan Neja Ya Ki Halartar Bikin Ranar Ma’aikata, Ana Zargin Akwai Takun Saka
Siyasa

Mataimakin Gwamnan Neja Ya Ki Halartar Bikin Ranar Ma’aikata, Ana Zargin Akwai Takun Saka

1 week ago
‘Yan Siyasa Na Komawa APC Don Buƙatar Kansu, Ba Don Jama’a Ba – Dalung
Siyasa

‘Yan Siyasa Na Komawa APC Don Buƙatar Kansu, Ba Don Jama’a Ba – Dalung

1 week ago
Next Post
Gwamnatin Tarayya Ta Amince Da Kashe Naira Tiriliyan 4.2 Don Aikin Manyan Hanyoyi

Gwamnatin Tarayya Ta Amince Da Kashe Naira Tiriliyan 4.2 Don Aikin Manyan Hanyoyi

LABARAI MASU NASABA

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

May 9, 2025
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

May 9, 2025
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

May 9, 2025
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

May 9, 2025
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.