• English
  • Business News
Friday, September 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sabbin Haraji: Yadda ‘Yan Bindiga Ke Tilasta Wa Jama’a Biyan Miliyoyin Kuɗi A Zamfara

by Sadiq
5 months ago
in Manyan Labarai
0
Gwamnatin Zamfara Ta Sanya Dokar Hana Fita A Fadin Jihar 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A Jihar Zamfara, wani bincike ya nuna yadda ‘yan bindiga ke tilasta wa mazauna wasu garuruwa biyan haraji don samun damar rayuwa ba tare da kai musu hari ba. 

Binciken wanda jaridar Daily Trust, ta gudanar ya nuna yadda matsalar tsaro ke ƙara ta’azzara a yankunan.

  • Gwamna Zulum Ya Ƙaddamar Da Aikin Gina Titi Da Gadar Sama Ta Huɗu A Borno 
  • Inganta Kiwon Lafiya: Gwamna Buni Ya Ziyarci Sashen Koyar Da Kwararrun Likitoci A Damaturu

Wannan lamari ya jefa mutane cikin tsananin fargaba da matsin tattalin arziƙi.

Rahoton ya nuna cewa tun daga watan Janairun 2025 zuwa yanzu, al’ummar yankunan sun riga sun biya kimanin Naira miliyan 500 ga ƙungiyoyin ‘yan bindiga domin tsira da rayukansu.

A cikin watan Janairu kaɗai, jagoran ‘yan bindiga da aka kashe, Isuhu Yellow, ya ƙaƙaba wa mutane harajin Naira miliyan 172.7 a kan ƙauyuka 25 tare da tilasta musu ba da kayan amfanin gona.

Labarai Masu Nasaba

NECO 2025: Gwamnan Kano Ya Bayyana Bayanai Ba Daidai Ba

‘Yancin Kananan Hukumomi: Yadda Gwamnoni Suke Kawo Cikas

Garuruwan da aka fi tsananta wa harajin sun haɗa da Gijinzama da aka tilasta musu biyan Naira miliyan 8.5, Dakolo da aka karɓi Naira miliyan 5 da buhun wake 20, sai Kibari da Kunchin Kalgo da suka biya Naira miliyan 20, Sungawa da Naira miliyan 15, da kuma Yalwa da aka tilasta su biyan Naira miliyan 2.7.

Bayan rasuwar Isuhu Yellow, wani ƙasurgumin jagoran ‘yan bindiga mai suna Dogo Gide ya sa harajin Naira miliyan 100 a kan ƙauyuka 23 da ke ƙaramar hukumar Tsafe.

A ƙarshen makon da ya gabata kuma, mazauna ƙauyen Dankurmi a ƙaramar hukumar Maru sun fuskanci sabon harajin Naira miliyan 60.

Wani mazaunin ƙauyen Dan Jibga, Muhammad Dogo, ya bayyana cewa bayan kashe mutane biyu a Gama Lafiya, an ƙaƙaba wa yankin harajin Naira miliyan 10.

Haka kuma, haraji ya ci gaba da yaɗuwa a Unguwar Tofa (Naira miliyan 26.6), Makera (Naira miliyan 15), Sungawa (Naira miliyan 20), Rakyabu (Naira miliyan 7), Yalwa (Naira miliyan 8), Mai Saje (Naira miliyan 11), da Langa-Langa (Naira miliyan 20 zuwa 30).

Sauran yankunan da ‘yan bindigar suka ƙaƙaba wa haraji sun haɗa da Gidan Dawa, Rijiyar Tsakar Dawa, Dan Jibga da kuma Bilbis. Malam Ibrahim Maru, wani mazaunin karamar hukumar Maru, ya ce matsalar ta’addanci a yankin na ƙara ta’azzara fiye da da.

Lamarin na nuna irin ƙalubalen da jama’a ke fuskanta a hannun masu aikata laifuka, wanda ke buƙatar kulawar gaggawa daga gwamnati da hukumomin tsaro.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: HarajiMatsalar TsaroYan bindigaZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

’Yansanda Sun Kama ‘Yar Shekara 40 Bisa Zargin Yi Wa Almajiri Fyaɗe A Bauchi

Next Post

Rashin Jituwa Tsakanin Amurka Da China Na Iya Jefa Tattalin Arziƙin Duniya Cikin Hatsari – IMF

Related

NECO 2025: Gwamnan Kano Ya Bayyana Bayanai Ba Daidai Ba
Manyan Labarai

NECO 2025: Gwamnan Kano Ya Bayyana Bayanai Ba Daidai Ba

10 hours ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Yadda Gwamnoni Suke Kawo Cikas
Manyan Labarai

‘Yancin Kananan Hukumomi: Yadda Gwamnoni Suke Kawo Cikas

12 hours ago
Kwankwaso na Tattaunawa da Shugaban APC Nentawe A Shirye-shiryen Sauya Sheƙa
Manyan Labarai

Kwankwaso na Tattaunawa da Shugaban APC Nentawe A Shirye-shiryen Sauya Sheƙa

13 hours ago
Ya Kamata Karancin Malamai A Duniya Ya Zama Darasi Ga Nijeriya
Manyan Labarai

Ya Kamata Karancin Malamai A Duniya Ya Zama Darasi Ga Nijeriya

14 hours ago
Sojoji Sun Kama ‘Yan Ta’adda 25, Sun Ceto Mutum 16 Da Aka Sace
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama ‘Yan Ta’adda 25, Sun Ceto Mutum 16 Da Aka Sace

23 hours ago
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano
Al'ajabi

Matashi Ya Kashe Kakanninsa Kan Abinci A Kano

1 day ago
Next Post
Rashin Jituwa Tsakanin Amurka Da China Na Iya Jefa Tattalin Arziƙin Duniya Cikin Hatsari – IMF

Rashin Jituwa Tsakanin Amurka Da China Na Iya Jefa Tattalin Arziƙin Duniya Cikin Hatsari – IMF

LABARAI MASU NASABA

Katsina Za Ta Ɗauki Nauyin Karatun Mahaddata Alƙur’ani – Gwamna Radda

Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Katsina: Nasara Ko Matsala?

September 26, 2025
Kasar Sin Na Farin Cikin Ganin Kamfanoni Suna Gudanar Da Shawarwarin Kasuwanci Da Kyau Bisa Ka’idojin Kasuwa

Kasar Sin Na Farin Cikin Ganin Kamfanoni Suna Gudanar Da Shawarwarin Kasuwanci Da Kyau Bisa Ka’idojin Kasuwa

September 26, 2025
An Gano Cututtuka Uku Da Suka Ta Da Hankalin Hukumomin Lafiya A Nijeriya

An Gano Cututtuka Uku Da Suka Ta Da Hankalin Hukumomin Lafiya A Nijeriya

September 26, 2025
Kasar Sin Ta Yi Alkawarin Bayar Da Sabuwar Gudummawa Dangane Da Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya

Kasar Sin Ta Yi Alkawarin Bayar Da Sabuwar Gudummawa Dangane Da Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya

September 26, 2025
Membobin Tawagar Koli Ta Sin Sun Ziyarci Jami’ai Da Gidajen Al’umma A Yankunan Jihar Xinjiang

Membobin Tawagar Koli Ta Sin Sun Ziyarci Jami’ai Da Gidajen Al’umma A Yankunan Jihar Xinjiang

September 26, 2025
Akwai Bukatar Sin Da Amurka Su Lalubo Hanya Mafi Dacewa Ta Tafiya Tare A Sabon Zamani

Akwai Bukatar Sin Da Amurka Su Lalubo Hanya Mafi Dacewa Ta Tafiya Tare A Sabon Zamani

September 26, 2025
Mazauna Kuyello A Jihar Kaduna Na Cikin Zullumin Bayyanar ‘Yan Ta’addar Ansaru

Gwamnati Ta Kafa Kwamitin Bincike A Kan Fashewar Wani Abu A Kaduna

September 26, 2025
An Samu Manyan Sauye-Sauye Na Zamani A Jihar Xinjiang Cikin Shekaru 70

An Samu Manyan Sauye-Sauye Na Zamani A Jihar Xinjiang Cikin Shekaru 70

September 26, 2025
Trump Ya Haramta Wa Jami’an Nijeriya Masu Cin Hanci Da Rashawa Shiga Amurka

Trump Ya Haramta Wa Jami’an Nijeriya Masu Cin Hanci Da Rashawa Shiga Amurka

September 26, 2025
Gwamnatin Kogi Ta Yi Haɗin Gwuiwa Don Fara Fitar Da Amfanin Gona

Gwamnatin Kogi Ta Yi Haɗin Gwuiwa Don Fara Fitar Da Amfanin Gona

September 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.