• English
  • Business News
Saturday, October 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mayar Da Hankali A Aikin Farfado Da Kwararrun Asibitocin Gwamnatin Tarayyya

by Leadership Hausa
4 months ago
in Manyan Labarai
0
Mayar Da Hankali A Aikin Farfado Da Kwararrun Asibitocin Gwamnatin Tarayyya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bayanin da Ministan Ilimi Dakta Tunji Alausa, ya yin a cewa, Shugaban Kasa Ahmed Tinubu, ya amince da kasafin Naira biliyan 110, domin a sabunta kayan aiki a Asibitin Kwararru na Gwamnatin Tarayya18, tabbas wannan abin yabawa ne.

Dakta Tunji ya yi bayani dalla-dalla kan yadda za a yi amfani da kudin, inda ya ce, za a yi amfani da Naira biliyan 70, wajen yiwa Makarantun koyar da aikin likita don mayar da su, daidai da irin na matakin kasa da kasa.

  • Darussan Koyi Daga Salon Bunkasa Kasa Na Sin
  • Ƙungiyar ’yan Majalisar Dokokin Ƙasa Ta APC Ta Amince Da Takarar Tinubu A ZaÉ“en 2027 

Kazalika, ya sanar da cewa, za a kuma yi amfani da Naira biliyan 15, wajen domin gina sabbin dakunan kwanan dalibai.

Tunji, har ila yau, ya bayyana cewa, za a kuma bai wa jami’oin kasar, guda 76, wasu somin tabin kudade, na tafiyar da cibiyoyin lafiyarsu da kuma kara yawan gurben daukar dalibai masu son karo karatun kwarrun kiwon lafiya.

Bugu da kari, duk a cikin wannan shirin, ya hada da, kafa dakunan yin gwaje-gwaje guda takwas, inda ko wanne Asibitin kwararru na Gwamnatin Tarayya, zai samu Naira biliyan hudu, domin samar da kyakyawan yanayi na karatu, ga kwararrun kiwon lafiya, musamman domin a rage kashe kudade, zuwa tura su ketare, domin su samu horo.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Zai Ziyarci Jos Domin Halartar Jana’izar Mahaifiyar Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa

PENGASSAN Ta Yi Watsi Da Tayin Dangote Na Biyan Ma’aikata Albashin Shekaru 5 Ba Tare Da Yin Aiki Ba

Matakin da Gwamnatin ta dauka, na son yin amfani da Gidauniyar TETFund, domin yin wannan aikin, babban abin jinjinawa ne, wanda idan har ba a samu wata gazawa ba, kamar a sauran ayyukan baya, musamman duba da cewa, Giduaniyar ta samu shedar cewa, ba a santa da gazawa, wajen wanzar da ayyukan da shirye-shiyen da ta sanya a gaba, kan batun ganin an inganta karatu a jami’oin kasar.

Kazalika, Ministan ya ce, daukacin aikin shi ne, domin a dakile yawan ficewar da kwararrun Likitocin kasar ne yi ne, zuwa ketere domin neman aiki, wanda hakan zai sanya, a ciki gaba da raike su a kasar nan, domin su yi aki a cikin kasar.

A karkashin aikin, za a kuma tabbatar da an samar da kayan aiki da samar da masu da karin kudade da kuma kara inganta yanayin mai kyau, da za su gudanar da ayyukansu, na duba marasa lafiya.

Alausa ya ci gaba da cewa, daukin da za a samar a fannin na kiwon lafiyar kasar, za a samar da shi ne, ga manyan bangarorin kimiyya, samar samar da magunguna da na jinya.

A cearsa, za a wanzar da wannan zuba hannun jarin ne, a fannin na zuwa shekaru biyar wanda aka kiyasta, za a kashe kudin da ya kai Naira tiriliyan 1.5 wanda za iya cimma hakan ne, ta hanyar wanzar da shiye-shiyen.

Sai dai, tun fil azala, kalubalen da kasar ke fuskanta shi ne, na Nijeriya na yin sakaci, wajen rashin wanzar da shirye-shiyen da aka dauka

Karin wani abin takaicin shi ne, fannin kiwon lafiyar kasar, musamman a kwararrun Asibitocin, sun koma tamkar abin damauwa ga ‘yan Nijeriya da kuma su kwararrun Likitocin, duba da yadda aka yi watis da ba su kulawar da ta kamata da yawan samun aikata badakalar cin hanci da rashawa, wanda hakan ya kara durkusar da fannin na kiwon lafiyar, wanda kuma hakan ya janyo, ba sanar inganciyyar kula da kiwon lafiyar da ya dace da kuma samar da ilimantar wa.

A nan za mu iya cewa, ya kamata Gwamnati baya ga samar da kayan aiki a Asibitocin, t ya kuma zama wajbi, ta zabo wasu Makarantun horas da kwararun Likitoci domin a daga darajar Makarantun.

Kwararrun Asibitocin kasar nan dai, sun jima da lalacewa da rashin ingantattun kayan aiki duba da cewa, ba su da Gadajen kwantar da marasa lafiya da suka wuce, goma kacal.

Akasarin ‘yan Nijeriya da ke bukatar a duba lafiyarsu, suna yin tururuwa zuwa kwararrun Asibitocin kasar, amma matsalar, suna shafe awowi, domin neman Gadon da za a kwantar da su don su yi jinya.

A wasu lokacin samun Asibtin, ya danganta ne da irin karfin iko da mai bukatar yake da shi.

Domin a dakile wannan matsalar, muna kira ga Gwamnati da mahukunatn irin wadannan kwararrun Asibitocin na Gwamnati, da su tabbtar da suna tattala kudaden da ake ware masu, a cikin kasafin kudin kasa, ba wai kawai batun yiwa Asibitocin garanbawul bane, amma a samar da kayan aiki na zamani, musamman mayar da hankali kan jin dadi da walwalar kwararn Likitocin.

Hakazalika, dole ne Gwamnati ta tabbatar da wanzar da samar da ingantaccen albashi, da samar da kyakyawan yanyin aikin aiki na kwararun Likitocin kasar, wanda hakan zai ba su damar samar da sakamako mai kyau, da ake bukata a fannin.

A saboda wadannan dalilan, ya zama wajibi, Gwamnatin Tarayya da rinka yin aiki kafada da kafada da kwararrun mahukuntan kiwon lafiya da sauran amsu ruwa da tsaki domin a samar da wata manhaja kan wannan aikin tare da cimma kudurin da aka sanya a gaba, kan lokaci.

Ya kamata a zuba hannun jari wajen bai wa kwararrun Likito horo domin a inganta kwarewarsu da kuma walwalarsu.

Bugu da kari, akwai bukatar a wadatar da Asibitocin kasar da kayan aiki na zamani, musamman domin a samu damar ci gaba da duba lafiyar marasa lafiya da kuma ilimantar da kwararrun Likitocin.

Ya kuma wajaba a samar da kayaan aiki na zamani da za a rinka duba manyan larorin cuttuka, kamar irinsu, Cutar Daji, wanda hakan zai sanya, masu irin wadannan larorin, ba sai sun fita zuwa Asibicin da ke ketare, domin neman lafiya ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Asibitoci
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Sama Jannatin Shenzhou-20 Sun Kammala Aiki A Wajen Tashar Sararin Samaniyar Kasar Sin

Next Post

Yadda Tabarbarewar Tsaro Ta Kara Yawan Yaran Da Ba Sa Zuwa Makaranta

Related

Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Tinubu Zai Ziyarci Jos Domin Halartar Jana’izar Mahaifiyar Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa

18 hours ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

PENGASSAN Ta Yi Watsi Da Tayin Dangote Na Biyan Ma’aikata Albashin Shekaru 5 Ba Tare Da Yin Aiki Ba

1 day ago
NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja
Manyan Labarai

NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja

1 day ago
Nijeriya A Shekara 65: Kwan-gaba Kwan-baya A Sha’anin Tsaro Da Siyasa Da Zamantakewa
Manyan Labarai

Nijeriya A Shekara 65: Kwan-gaba Kwan-baya A Sha’anin Tsaro Da Siyasa Da Zamantakewa

1 day ago
Katsina Za Ta Ɗauki Nauyin Karatun Mahaddata Alƙur’ani – Gwamna Radda
Manyan Labarai

Ina Aka Kwana Batun Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Dazukan Jihar Katsina?

1 day ago
Dubban Matasan Kano Sun Yi Zanga-zangar Lumana Domin Goyon Bayan CP AI Bakori
Manyan Labarai

Dubban Matasan Kano Sun Yi Zanga-zangar Lumana Domin Goyon Bayan CP AI Bakori

2 days ago
Next Post
Yadda Tabarbarewar Tsaro Ta Kara Yawan Yaran Da Ba Sa Zuwa Makaranta

Yadda Tabarbarewar Tsaro Ta Kara Yawan Yaran Da Ba Sa Zuwa Makaranta

LABARAI MASU NASABA

Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

October 4, 2025
An Nada Adamar Kamaye Sarautar Jakadiya A Kasar Ghana

An Nada Adamar Kamaye Sarautar Jakadiya A Kasar Ghana

October 4, 2025
Illolin Da Ke Tattare Da Mallaka Wa Kananan Yara Wayar Hannu

Illolin Da Ke Tattare Da Mallaka Wa Kananan Yara Wayar Hannu

October 4, 2025
Ƴar Wasan Gaban Nijeriya, Ifeoma Onumonu Ta Yi Ritaya

Ƴar Wasan Gaban Nijeriya, Ifeoma Onumonu Ta Yi Ritaya

October 4, 2025
Yadda Ake Lemon Tsamiya (Tamarin Juice)

Yadda Ake Lemon Tsamiya (Tamarin Juice)

October 4, 2025
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

October 4, 2025
Yadda Za A Magance Amosanin Baki

Yadda Za A Magance Amosanin Baki

October 4, 2025
Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu

Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu

October 4, 2025
Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato

Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato

October 4, 2025
Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet

Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.