• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babu Wanda Zai Fice Daga NNPP Da Zai Girgiza Siyasar Kwankwaso – Kofa

by Sadiq
3 years ago
in Siyasa
0
Babu Wanda Zai Fice Daga NNPP Da Zai Girgiza Siyasar Kwankwaso – Kofa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon Dan Majalisar Tarayya na Kananan Hukumomin Kiru da Bebeji, Abdulmuminu Jibril Kofa, ya ce a matakin da ake babu wani dan siyasa da zai fice daga jam’iyyar NNPP da zai girgiza siyasar Kwankwaso.

Yayin wata hira da gidan talabijin na Channels, Kofa, ya bayyana zamansa mai magana da yawun yakin neman zaben dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP.

  • Da Dumi-Dumi: ‘Yansanda Sun Cafke Wani Dan Bindiga Dan Shekara 20 A Kaduna
  • Za Mu Sa Kafar Wando Daya Da Masu Fasa Bututun Mai

A kan batun sauyin sheka da ake tunanin Sanata Ibrahim Shekarau zai yi daga NNPP zuwa wata jam’iyyar, Kofa ya ce ko Sanatan ya sauya sheka, jam’iyyarsu za ta kai labari a 2023.

Kofa, ya ce a 2019 an ga aya a zaben Kano, inda duk manyan ‘yan siyasa suka tare a APC, amma Rabiu Kwankwaso ya nuna musu nauyinsa, don haka babu wani wanda zai iya kada NNPP, domin Kwankwaso ya rike siyasar Kano, a cewarsa.

“A 2019 abun takaici, dukkaninmu sai mu ka bi Ganduje, Shekarau, Kabiru Gaya, Barau Jibrin, Kawu Sumaila, duk wani babba a Kano ya bi Ganduje, Me ya faru? Kwankwaso shi kadai a gefe guda, ya doke mu a zaben gwamna. Abin da ya faru a zaben, abin da aka gani ne, amma a gaskiya ya ci zabe.

Labarai Masu Nasaba

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

“Saboda haka idan ana zawarcin Shekarau, me ake nema ne, na gagara fahimtar wannan. Babu wanda zai bar NNPP a Kano da zai jijjiga Kwankwaso.”

Kamar yadda gidan rediyon Nasara da ke Kano ya wallafa, ya ce, Kofa wanda ya wakilci Kiru da Bebeji a majalisar tarayya ya ce hakan bai nufin yana kokarin cin mutuncin tsohon gwamna Shekarau, illa martani ga rade-radin da ake yi na cewa Malam Shekarau na neman barin NNPP, yayin da wasu ke zargin ya sa labule da sauran ‘yan takarar 2023.

A makon da ya gabata ne dai rahotanni suka karade kafafen watsa labarai cewa Shekarau zai fice daga NNPP sakamakon gaza cika masa wasu alkawura, abin da Kwankwaso ya ce sam ba haka bane, kuma babu wata matsala a tsakaninsu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AbdulMumuni Jibrin KofakanoKwankwasoNNPPSauya ShekaShekarauSiyasa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Da Dumi-Dumi: ‘Yansanda Sun Cafke Wani Dan Bindiga Dan Shekara 20 A Kaduna

Next Post

Da Dumi-Dumi: An Kori Shugaban Jam’iyyar APC Na Jihar Enugu Daga Jam’iyyar

Related

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki
Manyan Labarai

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

4 days ago
Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike
Siyasa

Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

5 days ago
Sulhun PDP Ya Haɗu Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya
Siyasa

Sulhun PDP Ya Haɗu Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya

1 week ago
‘Aikin Yan Uba Ne’ — Yahaya Bello Ya Karyata Zargin Sha’awar Takarar Shugaban Kasa A 2027
Siyasa

‘Aikin Yan Uba Ne’ — Yahaya Bello Ya Karyata Zargin Sha’awar Takarar Shugaban Kasa A 2027

2 weeks ago
Sanata Adamu Aliero Ya Ƙaddamar Da Rabon Kayan Tallafi Ga Ƙananan Hukumomi Takwas A Kebbi
Labarai

Sanata Adamu Aliero Ya Ƙaddamar Da Rabon Kayan Tallafi Ga Ƙananan Hukumomi Takwas A Kebbi

2 weeks ago
PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe
Siyasa

PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe

3 weeks ago
Next Post
Da Dumi-Dumi: An Kori Shugaban Jam’iyyar APC Na Jihar Enugu Daga Jam’iyyar

Da Dumi-Dumi: An Kori Shugaban Jam'iyyar APC Na Jihar Enugu Daga Jam'iyyar

LABARAI MASU NASABA

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.