Hukumar hasashen yanayi ta ƙasa (NiMet) ta fitar da hasashen sauyin yanayi na kwanaki uku, inda ta bayyana cewa za a fuskanci ruwan sama da hadari tun daga Litinin zuwa Laraba a sassa daban-daban na Nijeriya.
A cewar NiMet, ranar Litinin za a samu hazo da ruwan sama da safe a wasu sassan jihohin Taraba, Kaduna, Gombe, Bauchi, Kebbi, Sokoto, Katsina, Jigawa da Kano a Arewa. Daga bisani a rana, za a ci gaba da samun hadari da ruwan sama a jihohin Taraba, Kaduna, Sokoto, Borno, Kebbi da Zamfara.
- Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet
- Zafin Rana Zai Tsananta A Wasu Jihohin Nijeriya – NiMet
A yankin Arewa ta tsakiya, jihohin Abuja, Neja da Nasarawa za su fuskanci ruwan sama da hazo da safe. Yamma kuma za a samu hadari da ruwan sama a Filato, Abuja, Nasarawa, Kwara, Neja, Kogi da Benue.
A Kudu, za a fara da samun gajimare da ruwan sama a wasu sassan Ondo, Ogun, Edo, Ebonyi, Abia, Cross River, Rivers da Akwa Ibom. Daga bisani kuma, ana sa ran ruwan sama a Oyo, Ekiti, Osun, Lagos, Edo, Imo, Enugu, Delta da Bayelsa.
Ranar Talata, NiMet ta ce za a fuskanci hazo da ruwan sama da safe a jihohin Kano, Zamfara, Katsina, Bauchi, Gombe, Adamawa, Borno, Yobe da Taraba. Yamma kuma, za a samu ruwan sama a jihohin Taraba, Kebbi, Borno, Adamawa, Kaduna da Bauchi. Arewa ta tsakiya za ta ci gaba da hadari da ruwa a Abuja, Neja da Nasarawa, yayin da jihohin Kogi, Kwara da Filato za su bi sahu da rana.
Ranar Laraba, ruwan sama da hazo za su afkawa jihohin Zamfara, Adamawa, Kaduna, Sokoto, Kebbi da Taraba. Daga baya kuma, za a samu ruwan sama a jihohin Katsina, Bauchi da Sakkwato. Arewa ta rsakiya za ta fuskanci ruwan sama a Abuja, Nasarawa, Neja da Binuwe da safe, yayin da yamma za ta shafi Nasarawa, Filato, Kwara da Kogi.
A Kudu, ana hasashen ruwan sama da safe a Ogun, Ondo, Oyo, Edo, Enugu, Ebonyi, Cross River, Rivers da Akwa Ibom, sannan daga bisani a rana, za a sami ruwan sama a fadin yankin.
NiMet ta gargjama’a su ɗauki matakan kariya, musamman inda hadari zai faru, domin iska mai ƙarfi na iya gabatar da haɗari. An shawarci mutane su guji tuƙi a lokacin ruwan sama mai ƙarfi, su cire na’urori daga soket, su guji tsayuwa kusa da manyan itatuwa, sannan masu jirgin sama su nemi rahoton yanayi daga NiMet kafin tafiya. Ana kuma shawarci jama’a su dinga bin sahihan bayanan yanayi daga shafin NiMet:
www.nimet.gov.ng.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp