Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano ya bar filin jirgin sama na Malam Aminu Kano a daren ranar Lahadi yana jagorantar wata tawagar manyan mutane domin halartar jana’izar marigayi hamshakin dan kasuwa kuma dattijon jihar, Alhaji Aminu Alhassan Dantata a birnin Madina na kasar Saudiyya wanda ya rasu da sanyin safiyar Asabar a birnin Abu Dhabi na kasar Dubai.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar.
- Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada
- Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume
Gwamnan yana tare da Mai Martaba Sarkin Kano, Khalifa Muhammadu Sanusi II, tare da Gwamnan Jihar Jigawa Alhaji Umar Namadi, tsohon Gwamna Barrista Ali Saad Birnin Kudu da sauran manyan jami’an gwamnati da manyan mutane a jihar.
Da yake jawabi jim kadan kafin tashinsa a filin jirgin sama na Malam Aminu Kano, Gwamna Yusuf ya bayyana marigayi Dantata a matsayin uba ga mutane da yawa, wanda karamcinsa da sadaukarwarsa ya wuce iyaka.
Gwamnan ya jaddada cewa, zuwan tawagar a Madina shaida ce ta matukar mutuntawa da jama’a da gwamnatin jihar Kano suke yi masa na gadon alkairai da ya bari kuma a matsayinsa na dattijon jihar.
Ana sa ran jana’izar da za a yi a birnin Madina, za ta samu halartar wakilan jiha da na tarayya, da ‘yan uwa, ‘yan kasuwa, malaman addinin Islama, da masoya daga sassan duniya baki daya, tare da yin addu’ar Allah ya jikansa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp