• English
  • Business News
Saturday, August 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

by Bello Hamza and Sulaiman
3 weeks ago
in Tattalin Arziki
0
Dangote
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Rukunin Kamfanonin Dangote, Alhaji Aliko Dangote, ya jinjinawa Hukumar Kula da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Kasa NPA.

Dangote, ya yabawa NPA ne, bisa kokarinta na wanzar da tsarin Gwamnatin Tarayya na sayar da Danyen Mai da kuma Man Fetur, da sauran dangogin Man Fetur da ake tacewa a cikin gida Nijeriya, kan farashin Naira.

  • Al’umma Na Kokawa Kan Tsadar Kayan Miya A Sassan Kasar Nan
  • Wata Motar Tankar Mai Ta Kama Da Wuta Tare Da Kone Wasu Motoci A Ibadan, Jihar Oyo

A saboda hakan ne, Dangote, ya bayar da kyautar sabuwar motar Bas kirar Coaster, domin karfafawa kwamitin da zai aikin, guiwa, wanda a turance, ake kira da One-Stop-Shop.

A cikin wata wasika da Dangote ya rattabawa hannu, ya kuma bayar da tabbcin cewa, Kamfaninsa zai ci gaba da samar da hanyoyin da zai rinka taimakwa kwamntin, domin ya samu gudanar da aikin da aka dora masa, bisa umarnin Fadar Shugaban kasa.

“Mun ammana da cewa, wannan motar Bas din, kwamitin zai yi aiki da ita yadda ya kamata, duba da cewa, Kamfanin na, zai ci gaba da bai wa kwamtin goyon baya,” Inji Dangote.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Za Ta Aiwatar da Shirin Daƙile Sulalewar Kuɗaɗen Haraji

Sabon Shugaban Matatar Dangote Ya Bayyana Shirin Faɗaɗa Ayyukanta

Idan za a iya tunawa, Shugaban karamin kwamitin na wanzar da sayar da Danyen Man da kuma sauran dangogin Man Fetur da ake tacewa kasar kan farashin Naira Zacch Adedeji, ya jabawa hukumar ta NPA, bisa samar da aikin a cikin sauki

Adedeji, ya yi wannan yabon ne, lokacin da ya jagoranci tawagar kwamtin zuwa hukumar ta NPA, inda kuma ya yabawa tawagar kwamtin, da ke a karkashin NPA, kan gundunmawar da take ci gaba da bayar wa, domin a samu cimma burin da aka sanya a gaba.

“Mun lura da cewa, babu shakka wannan kokarin na hukumar ta NPA ya nuna irin kishin da hukumar take da shi a zahir, wajen cimma nasarar da aka sanya a gaba, “A cewar Adedeji.

“Ina mai kara maku kwarin guiwar cewa, kar ku gajiya wajen cimma burin da aka sanya a gaba, musamman domin a samu cin nasarar aikin, kuma muna mika godiyar mu, ga sauran hukumomin da suke ci gaba da bayar da goyon bayansu”. In ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Next Post

2027: Gangamin ‘Yan Adawa Ya Sa APC Fafutukar Neman Mafita

Related

Gwamnatin Tarayya Za Ta Aiwatar da Shirin Daƙile Sulalewar Kuɗaɗen Haraji
Tattalin Arziki

Gwamnatin Tarayya Za Ta Aiwatar da Shirin Daƙile Sulalewar Kuɗaɗen Haraji

6 days ago
Sabon Shugaban Matatar Dangote Ya Bayyana Shirin Faɗaɗa Ayyukanta
Tattalin Arziki

Sabon Shugaban Matatar Dangote Ya Bayyana Shirin Faɗaɗa Ayyukanta

7 days ago
Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa
Tattalin Arziki

Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa

1 week ago
Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA
Tattalin Arziki

Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

2 weeks ago
Afrika Ta Zama Kasuwar Sayar Da Man Fetur Mara Inganci – Dangote
Tattalin Arziki

Afrika Ta Zama Kasuwar Sayar Da Man Fetur Mara Inganci – Dangote

3 weeks ago
NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma
Tattalin Arziki

NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma

4 weeks ago
Next Post
APC

2027: Gangamin ‘Yan Adawa Ya Sa APC Fafutukar Neman Mafita

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

August 8, 2025
Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza

Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza

August 8, 2025
Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?

Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?

August 8, 2025
Nijeriya Ta Horar Da Likitoci 360 Don Magance Mutuwar Mata Masu Juna Biyu

Nijeriya Ta Horar Da Likitoci 360 Don Magance Mutuwar Mata Masu Juna Biyu

August 8, 2025
Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe

Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe

August 8, 2025
Bashir Ojulari: Me Ya Sa Ake Tsoron Gaskiya Ta Yi Aiki A NNPC? 

Bashir Ojulari: Me Ya Sa Ake Tsoron Gaskiya Ta Yi Aiki A NNPC? 

August 8, 2025
Gwamnatin Kaduna Ta Amince Da Hutun Wata 6 Ga Mata Masu Shayarwa

Gwamnatin Kaduna Ta Amince Da Hutun Wata 6 Ga Mata Masu Shayarwa

August 8, 2025
’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

An Hallaka Manomi, An Kashe Shanu Da Tumakai A Wani Sabon Rikici A Bogoro

August 8, 2025
An Bude Taron Mutum-Mutumin Inji Na Duniya Na 2025 A Yau Juma’a

An Bude Taron Mutum-Mutumin Inji Na Duniya Na 2025 A Yau Juma’a

August 8, 2025
Bango Ya Kashe Mutum 6, Ya Raunata Wasu A Katsina

Bango Ya Kashe Mutum 6, Ya Raunata Wasu A Katsina

August 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.