ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Ceto Sauran Mutanen Da Aka Yi Garkuwa Da Su Daga Ukuba, In Ji Iyalan Al-Kadiriyah

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Ceto

LABARAI MASU NASABA

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

An Kama Sojoji Biyu A Legas Kan Alaka Da Sarrafa Magungunan Jabu

ADVERTISEMENT

Iyalan Al-Kadiriyah na yankin Okekere da ke Ilorin, Jihar Kwara, sun yi kira da a hada karfi da karfe domin ganin an sako wadanda aka yi garkuwa da su a fadin kasar nan.

Iyalan a yayin da suke murnar sakin ‘ya’yansu mata da masu garkuwa da su suka yi, sun bukaci shugabanin Nijeriya da ‘yan kasar da kada su yi watsi da wadanda har yanzu ake garkuwa da su.

  • Tsadar Magunguna Na Barazana Ga Rayukan Majinyata A Nijeriya
  • Kofin Afirka 2023: Yadda Manyan Kasashe Ke Tafka Abin Kunya

Biyar daga cikin ’yan uwa mata na ahalin Al-Kadriyar shida da aka yi garkuwa da su a Bwari da ke Abuja a farkon watan Janairu, sun samu ‘yanci.

Haka kuma, wani da aka yi garkuwa da shi, Suleiman Sabo, an kubutar da shi daga hannun masu garkuwa da mutane a Sauka, daura da titin filin jirgin sama, Abuja.

Jami’an rundunar ‘yansanda da ke yaki da masu garkuwa da mutane a Babban Birnin Tarayya, a kokarin hadin gwiwa tare da sojojin Nijeriya, sun ceto mutanen da aka yi garkuwa da su a yankin Zuma 1 da ke Karamar Hukumar Bwari, wadanda aka yi garkuwa da su a ranar 2 ga Janairun 2024.

Da take tabbatar da rahoton, kakakin rundunar ‘yansandan Babban Birnin Tarayya Abuja, SP Josephine Adeh, ta ce ‘yansandan sun yi nasarar ceto wadanda lamarin ya rutsa da su a dajin Kajuru a Jihar Kaduna da misalin karfe 11:30 na dare.

A cikin wata sanarwa da suka fitar, ta hannun daya cikin ahalin Al-Kadiriyah Sherifdeen, sun ce: “A wannan lokacin na murna, kar mu manta da wadanda har yanzu suke fuskantar wahalhalu a hannun ‘yan bindiga, mu ci gaba da yi musu addu’ar Allah ya dawo da su lafiya. Ya zama wajibi mu a matsayinmu na al’umma mu tallafa wa juna da kuma daukaka juna a lokutan da suke shan wahala.”

Sherifdeen ya yi kira da a yi addu’o’in samun lafiya ga rayukan wadanda suka mutu a hannu masu garkuwa da mutane.

Ya kuma mika godiyarsa ga jami’an tsaro, hukumomi, da duk wadanda suka jajirce wajen ganin an ceto ‘ya’ya matan.

Har ila yau, shugaban kungiyar ‘yan asalin Ilorin Masarautar IEDPU na kasa, Alhaji Abdulmumini AbdulMalik, ya sake jaddada bukatar gwamnati a dukkan matakai na tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin ‘yan kasa.

Ya gode wa Gwamnan Jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazak, Sarkin Ilorin, Alhaji Ibrahim Sulu-Gambari, Tsohon Ministan Sadarwa da Tattalin Arziki na Zamani, Farfesa Issa Ali Patanmi da sauran al’ummar Masarautar Ilorin, musamman, don goyon baya da addu’o’in da aka bai wa iyalan Al-Kadiriyah a lokacin da aka bayyana irin manancin halin da suka tsinci kansu.”

LEADERSHIP Hausa ta bayar da rahoton cewa an sace ‘yan matan ne tare da mahaifinsu da kuma wasu mazauna unguwar, inda nan take aka sako mahaifinsu aka umarce su da ya biya kudin fansa kimanin Naira miliyan 60 ga yaran.

Daya daga cikin ‘yan uwa mata mai suna Nabeeha, daga baya masu garkuwa da mutane suka kashe ta saboda ba su biya kudin fansar da gaggawa.

A halin da ake ciki kuma, a yayin aikin ceton, an kama wani da ake zargi mai suna Muhammad Abel, mai shekaru 32, daga Jihar Kogi, tare da kwato bindigar LAR guda daya da harsashi guda goma 10.

A jiya kuma aka samu rahoton an sako wasu mutum bakwai da aka yi garkuwa da su a rukunin gidajen Sagwari da ke Karamar Hukumar Bwari a Babban Birnin Tarayya Abuja.

An sace su ne kwanaki da suka wuce lokacin da ‘yan bindiga suka kai farmaki a gidan da misalin karfe 8 na dare

Wata daga cikin wadanda abin ya shafa, Talatu Salihu, daliba mai matakin digiri na 500 akan Laburare da Kimiyyar Yada Labarai, Jami’ar Bayero Kano (BUK)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
An Kama Sojoji Biyu A Legas Kan Alaka Da Sarrafa Magungunan Jabu
Kotu Da Ɗansanda

An Kama Sojoji Biyu A Legas Kan Alaka Da Sarrafa Magungunan Jabu

December 20, 2025
An Ceto Wasu Samari 11 ‘Yan Jihar Jigawa Daga Hannun Masu Fataucin Mutane
Kotu Da Ɗansanda

An Ceto Wasu Samari 11 ‘Yan Jihar Jigawa Daga Hannun Masu Fataucin Mutane

December 20, 2025
Next Post
Jariri Ya Yi Batan Dabo A Asibitin Waziri Gidado Da Ke Kano

Jariri Ya Yi Batan Dabo A Asibitin Waziri Gidado Da Ke Kano

LABARAI MASU NASABA

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025
Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

December 20, 2025
An Nuna Jigo Da Tambarin Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Shekarar 2026 A Moscow

An Nuna Jigo Da Tambarin Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Shekarar 2026 A Moscow

December 20, 2025
Auren Da Ya Fi Auren Gidan Daula Dadi Ga Mace

Auren Da Ya Fi Auren Gidan Daula Dadi Ga Mace

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.