• English
  • Business News
Saturday, October 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Ceto Sauran Mutanen Da Aka Yi Garkuwa Da Su Daga Ukuba, In Ji Iyalan Al-Kadiriyah

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
A Ceto Sauran Mutanen Da Aka Yi Garkuwa Da Su Daga Ukuba, In Ji Iyalan Al-Kadiriyah
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

Iyalan Al-Kadiriyah na yankin Okekere da ke Ilorin, Jihar Kwara, sun yi kira da a hada karfi da karfe domin ganin an sako wadanda aka yi garkuwa da su a fadin kasar nan.

Iyalan a yayin da suke murnar sakin ‘ya’yansu mata da masu garkuwa da su suka yi, sun bukaci shugabanin Nijeriya da ‘yan kasar da kada su yi watsi da wadanda har yanzu ake garkuwa da su.

  • Tsadar Magunguna Na Barazana Ga Rayukan Majinyata A Nijeriya
  • Kofin Afirka 2023: Yadda Manyan Kasashe Ke Tafka Abin Kunya

Biyar daga cikin ’yan uwa mata na ahalin Al-Kadriyar shida da aka yi garkuwa da su a Bwari da ke Abuja a farkon watan Janairu, sun samu ‘yanci.

Haka kuma, wani da aka yi garkuwa da shi, Suleiman Sabo, an kubutar da shi daga hannun masu garkuwa da mutane a Sauka, daura da titin filin jirgin sama, Abuja.

Jami’an rundunar ‘yansanda da ke yaki da masu garkuwa da mutane a Babban Birnin Tarayya, a kokarin hadin gwiwa tare da sojojin Nijeriya, sun ceto mutanen da aka yi garkuwa da su a yankin Zuma 1 da ke Karamar Hukumar Bwari, wadanda aka yi garkuwa da su a ranar 2 ga Janairun 2024.

Da take tabbatar da rahoton, kakakin rundunar ‘yansandan Babban Birnin Tarayya Abuja, SP Josephine Adeh, ta ce ‘yansandan sun yi nasarar ceto wadanda lamarin ya rutsa da su a dajin Kajuru a Jihar Kaduna da misalin karfe 11:30 na dare.

A cikin wata sanarwa da suka fitar, ta hannun daya cikin ahalin Al-Kadiriyah Sherifdeen, sun ce: “A wannan lokacin na murna, kar mu manta da wadanda har yanzu suke fuskantar wahalhalu a hannun ‘yan bindiga, mu ci gaba da yi musu addu’ar Allah ya dawo da su lafiya. Ya zama wajibi mu a matsayinmu na al’umma mu tallafa wa juna da kuma daukaka juna a lokutan da suke shan wahala.”

Sherifdeen ya yi kira da a yi addu’o’in samun lafiya ga rayukan wadanda suka mutu a hannu masu garkuwa da mutane.

Ya kuma mika godiyarsa ga jami’an tsaro, hukumomi, da duk wadanda suka jajirce wajen ganin an ceto ‘ya’ya matan.

Har ila yau, shugaban kungiyar ‘yan asalin Ilorin Masarautar IEDPU na kasa, Alhaji Abdulmumini AbdulMalik, ya sake jaddada bukatar gwamnati a dukkan matakai na tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin ‘yan kasa.

Ya gode wa Gwamnan Jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazak, Sarkin Ilorin, Alhaji Ibrahim Sulu-Gambari, Tsohon Ministan Sadarwa da Tattalin Arziki na Zamani, Farfesa Issa Ali Patanmi da sauran al’ummar Masarautar Ilorin, musamman, don goyon baya da addu’o’in da aka bai wa iyalan Al-Kadiriyah a lokacin da aka bayyana irin manancin halin da suka tsinci kansu.”

LEADERSHIP Hausa ta bayar da rahoton cewa an sace ‘yan matan ne tare da mahaifinsu da kuma wasu mazauna unguwar, inda nan take aka sako mahaifinsu aka umarce su da ya biya kudin fansa kimanin Naira miliyan 60 ga yaran.

Daya daga cikin ‘yan uwa mata mai suna Nabeeha, daga baya masu garkuwa da mutane suka kashe ta saboda ba su biya kudin fansar da gaggawa.

A halin da ake ciki kuma, a yayin aikin ceton, an kama wani da ake zargi mai suna Muhammad Abel, mai shekaru 32, daga Jihar Kogi, tare da kwato bindigar LAR guda daya da harsashi guda goma 10.

A jiya kuma aka samu rahoton an sako wasu mutum bakwai da aka yi garkuwa da su a rukunin gidajen Sagwari da ke Karamar Hukumar Bwari a Babban Birnin Tarayya Abuja.

An sace su ne kwanaki da suka wuce lokacin da ‘yan bindiga suka kai farmaki a gidan da misalin karfe 8 na dare

Wata daga cikin wadanda abin ya shafa, Talatu Salihu, daliba mai matakin digiri na 500 akan Laburare da Kimiyyar Yada Labarai, Jami’ar Bayero Kano (BUK)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Rantsar Da Ododo A Matsayin Gwamnan Kogi

Next Post

Jariri Ya Yi Batan Dabo A Asibitin Waziri Gidado Da Ke Kano

Related

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi
Kotu Da Ɗansanda

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

4 hours ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

5 hours ago
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Farmaki Masu Safarar Muggan Kwayoyi A Sassan Nijeriya

1 week ago
‘Yansanda Sun Cafke Mutum Hudu Kan Satar Taransifoma A Makaranatar Kebbi
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Cafke Mutum Hudu Kan Satar Taransifoma A Makaranatar Kebbi

1 week ago
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da Ɗansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

1 month ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

1 month ago
Next Post
Jariri Ya Yi Batan Dabo A Asibitin Waziri Gidado Da Ke Kano

Jariri Ya Yi Batan Dabo A Asibitin Waziri Gidado Da Ke Kano

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu

Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu

October 4, 2025
Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato

Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato

October 4, 2025
Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet

Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet

October 4, 2025
Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

October 4, 2025
Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

October 4, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

October 4, 2025
Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

October 3, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Tinubu Zai Ziyarci Jos Domin Halartar Jana’izar Mahaifiyar Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa

October 3, 2025
MDD Ta Yi Alƙawarin Tallafa Wa Gidauniyar Malala Mai Rajin Inganta Ilimin ‘Ya’ya Mata

MDD Ta Yi Alƙawarin Tallafa Wa Gidauniyar Malala Mai Rajin Inganta Ilimin ‘Ya’ya Mata

October 3, 2025
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

October 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.