• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Dau Darasi Daga Asarar Dala Biliyan 100 Sakamakon Rikicin Arewa Maso Gabas

by Leadership Hausa
2 years ago
in Rahotonni
0
Arewa maso Gabas
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gidauniyar Yara ta Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF) ta bayar da wani rahoto da ya girgiza al’ummar Nijeriya da ma Duniya baki daya.

Rahoton ya bayyana cewa, Nijeriya ta yi asarar fiye da Dala Biliyan 100 a bangaren tattalin arziki a shekara 10 da aka yi ana tafka rikici a yankin Arewa maso Gabashin kasar, yakin da ‘yan ta’addan Boko Haram ke jagoranta.

  • An Kashe ‘Yan Ta’adda 41 Yayin Da Boko Haram Da ISWAP Suka Bai Wa Hammata Isla A Borno

Tabbas wannan bayanin ya ratsa al’umma Nijeriya ya kuma tayar da bukatar a sake tunani tare da nemo hanyar magance matsalar da ke haifar da wadannan rikice-rikice da suka ki ci suka ki cinyewa.

Rikicin da a halin yanzu ya yi shekaru ana tafkawa, don an fara ne a shekarar 2008 har zuwa lokacin da aka rubuta rahoton wato shekarar 2021, ya bar alamomi na tashin hankali a bangaren zamantakewa da tattalin arzikin Nijeriya gaba daya.

Rahoton ya kuma kara da cewa, an kashe mutum fiye da 35,000 tun da aka fara wannan rikici a shekarar 2009 lokacin da kungiyar Boko Haram ta kaddamar da gwagwarmayarta na hambarar da gwamnatin Nijeriya don kafa tsarin mulkin Musulunci.

Labarai Masu Nasaba

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

Rahoton na Majalisar Dinkin Duniya ya bayyana sakamakon da rikinci ya haifar ga al’umma tun daga rasa rayuka, raunata al’ummna da dama, rasa matsugunai da kuma yadda al’amarin ya shafi tattalin arzikn kasa gaba daya.

Wadannan su suka taru suka nemi durkusar da tattalin arzikin kasa abin da kuma bai kamata a yi banza da shi ko kuma a kawar da kai ba.

Rahoton ya kiyasta asarar da aka yi ga tattalin arzikin kasa da kuma irin yadda al’amarin ya durkusar da kokarin da gwamnatoci suka yi na bunkasaa tattalin arzikin yankin da ma Nijeriya baki daya.

Kiyasin da aka yi na asarar Dala Biliyan 100 yana nuna abubuwan da aka yi asara na wadanda za a iya gani da idanuwa da kuma asarorin da aka yi wasu matakai da ya kamata a dauka amma ba a dauka ba da kuma kubutar da mutane daga talaucin da ba a iya yi ba sakamakon rikice-rikicen.

Matsalolin da rikicin ya haifar bai takaita ga yankin Arewa maso Gabas kawai ba, duk da cewa daga nan ne rikicin ya samo asali, lamarin ya shafi dukkan kasar ne, kamar yadda rahoton ya nuna.

Koma baya da aka samu na tattalin arziki a yankin ya faru ne saboda yadda aka fuskanci rikice-rikicen ba tare da kaukautawa ba, wanda hakan ya shafi zaman lafiyar Nijeriya gaba daya.

A wannan lokaci da duniya ke zaman cude ni in cude ka, matsalolin da Nijeriya ke fuskanta yana iya shafar zaman lafiyan kasashe makabtanmu da ma yankin Afrika gaba daya.

Wakiliyar UNICEF a Nijeriya, Cristian Munduate, ta yi daidai inda ta bayyana cewa, koda an iya murkushe wannan tashin hankali to lallai barnar da tashin hankalin ya haifar zai dade ana ci gaba da jin radadinsa.

A ra’ayinmu in har ana son a yi maganin wannan matsalar, dole Nijeriya ta dauki matakai masu muhimmanci, na farko dole a dauki matakan kawo karshen rikicin tare da dawo da zaman lafiya a yankin Arewa maso Gabas tare da samar da yanayin yafiya a tsakanin al’umma da kuma tsugunar da wadanda yakin ya tarwatsa, ta haka za a samar da fahimtar juna a tsakanin al’umma, wanda kuma hakan zai kai ga samar da dawwamanmen zaman lafiya, sannan ta haka za a iya yin maganin matsalolin da rikicin ya haifar na tsawon shekara fiye da 10.

Bugu da kari kuma, zuba jari a bangaren ilimi da kiwon lafiya yana da matukar muhimmanci musamman ga yaran da rikicin ya raba da iyalansu da kuma gidajensu, haka yana da matukar muhimmanci.

Wannan jari da za a zuba ba wai kawai ya zama dole ba ne yana kuma da matukar muhimmanci a wajen samar da yara masu cikakkiyar lafiya da ilimi, hakan kuma shi ne ginshikin ci gaba da bunkasar kasar baki daya.

Haka kuma yana da muhimmanci a samar da wasu hanyoyin samun kudin shiga ga kasa, dogaro ga bangaren man fetur ba zai haifar da da mai ido ba ga Nijeriya. Dole Nijeriya ta nuna wasu hanyoyin samun kudaden shiga wanda zai samar mana da ci gaba a bangaren samar da ayyukan yi ga matasanmu da rage talauci a tsakanin al’umma.

Baya ga kokarin da ake yi a cikin gida, hadin kai da kungiyoyin kasashe waje yana da matukar muhimmanci. Dole Nijeriya ta nemi gudummawar abokan hulda na kasashen waje wajen neman yadda za a samu saukin kawo karshen rikicin da kuma yadda za a yi maganin abubuwan da rikicin ya haifar. Al’umma na da muradin ganin sun taimaka wa Nijeriya da hanyoyin magance matsalolin tare da samar da zaman lafiya don ta haka za a tabbatar da zaman kafiya a duniya baki daya.

A ra’ayinmu, wannan rahoton yana karfafa bukatar rungumar matakan kariya ne na kokarin kauce wa fadawa irin wannan rikicin a nan gaba. Samar da hanyoyin kare aukuwar rikici zai kai ga ceto rayuwar al’umma da kuma ceto tattalin arzikin kasa. Don haka bayanin cewa, an yi asarar fiye da Dala Biliyan 100 a rikincin yankin Arewa maso Gabas ya kamata ya farkar da mu, kuma hakan ya zama izna ga Nijeriya da ma Duniya baki daya a kan bukatar a rungumi hanyoyin kare aukuwar rikici ba wai sai wani abu ya faru ba a fara kame-kame.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan Boko Haram'Yan ta'addaMDDUNICEF
ShareTweetSendShare
Previous Post

Han Zheng Ya Yi Kira Ga Sin Da Amurka Da Su Kyautata Matakan Shawo Kan Sabani

Next Post

Wa Ya Yi Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Katsina?

Related

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
Rahotonni

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

18 hours ago
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

7 days ago
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
Rahotonni

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

7 days ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

2 weeks ago
Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi
Rahotonni

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

2 months ago
Janar Tiani Ya Fara Sabon Mulkin Shekaru Biyar A Nijar
Rahotonni

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

2 months ago
Next Post
'Yan Bindiga

Wa Ya Yi Sulhu Da 'Yan Bindiga A Katsina?

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.