• English
  • Business News
Monday, November 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Dau Darasi Daga Asarar Dala Biliyan 100 Sakamakon Rikicin Arewa Maso Gabas

by Leadership Hausa
2 years ago
Arewa maso Gabas

Gidauniyar Yara ta Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF) ta bayar da wani rahoto da ya girgiza al’ummar Nijeriya da ma Duniya baki daya.

Rahoton ya bayyana cewa, Nijeriya ta yi asarar fiye da Dala Biliyan 100 a bangaren tattalin arziki a shekara 10 da aka yi ana tafka rikici a yankin Arewa maso Gabashin kasar, yakin da ‘yan ta’addan Boko Haram ke jagoranta.

  • An Kashe ‘Yan Ta’adda 41 Yayin Da Boko Haram Da ISWAP Suka Bai Wa Hammata Isla A Borno

Tabbas wannan bayanin ya ratsa al’umma Nijeriya ya kuma tayar da bukatar a sake tunani tare da nemo hanyar magance matsalar da ke haifar da wadannan rikice-rikice da suka ki ci suka ki cinyewa.

Rikicin da a halin yanzu ya yi shekaru ana tafkawa, don an fara ne a shekarar 2008 har zuwa lokacin da aka rubuta rahoton wato shekarar 2021, ya bar alamomi na tashin hankali a bangaren zamantakewa da tattalin arzikin Nijeriya gaba daya.

Rahoton ya kuma kara da cewa, an kashe mutum fiye da 35,000 tun da aka fara wannan rikici a shekarar 2009 lokacin da kungiyar Boko Haram ta kaddamar da gwagwarmayarta na hambarar da gwamnatin Nijeriya don kafa tsarin mulkin Musulunci.

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

Rahoton na Majalisar Dinkin Duniya ya bayyana sakamakon da rikinci ya haifar ga al’umma tun daga rasa rayuka, raunata al’ummna da dama, rasa matsugunai da kuma yadda al’amarin ya shafi tattalin arzikn kasa gaba daya.

Wadannan su suka taru suka nemi durkusar da tattalin arzikin kasa abin da kuma bai kamata a yi banza da shi ko kuma a kawar da kai ba.

Rahoton ya kiyasta asarar da aka yi ga tattalin arzikin kasa da kuma irin yadda al’amarin ya durkusar da kokarin da gwamnatoci suka yi na bunkasaa tattalin arzikin yankin da ma Nijeriya baki daya.

Kiyasin da aka yi na asarar Dala Biliyan 100 yana nuna abubuwan da aka yi asara na wadanda za a iya gani da idanuwa da kuma asarorin da aka yi wasu matakai da ya kamata a dauka amma ba a dauka ba da kuma kubutar da mutane daga talaucin da ba a iya yi ba sakamakon rikice-rikicen.

Matsalolin da rikicin ya haifar bai takaita ga yankin Arewa maso Gabas kawai ba, duk da cewa daga nan ne rikicin ya samo asali, lamarin ya shafi dukkan kasar ne, kamar yadda rahoton ya nuna.

Koma baya da aka samu na tattalin arziki a yankin ya faru ne saboda yadda aka fuskanci rikice-rikicen ba tare da kaukautawa ba, wanda hakan ya shafi zaman lafiyar Nijeriya gaba daya.

A wannan lokaci da duniya ke zaman cude ni in cude ka, matsalolin da Nijeriya ke fuskanta yana iya shafar zaman lafiyan kasashe makabtanmu da ma yankin Afrika gaba daya.

Wakiliyar UNICEF a Nijeriya, Cristian Munduate, ta yi daidai inda ta bayyana cewa, koda an iya murkushe wannan tashin hankali to lallai barnar da tashin hankalin ya haifar zai dade ana ci gaba da jin radadinsa.

A ra’ayinmu in har ana son a yi maganin wannan matsalar, dole Nijeriya ta dauki matakai masu muhimmanci, na farko dole a dauki matakan kawo karshen rikicin tare da dawo da zaman lafiya a yankin Arewa maso Gabas tare da samar da yanayin yafiya a tsakanin al’umma da kuma tsugunar da wadanda yakin ya tarwatsa, ta haka za a samar da fahimtar juna a tsakanin al’umma, wanda kuma hakan zai kai ga samar da dawwamanmen zaman lafiya, sannan ta haka za a iya yin maganin matsalolin da rikicin ya haifar na tsawon shekara fiye da 10.

Bugu da kari kuma, zuba jari a bangaren ilimi da kiwon lafiya yana da matukar muhimmanci musamman ga yaran da rikicin ya raba da iyalansu da kuma gidajensu, haka yana da matukar muhimmanci.

Wannan jari da za a zuba ba wai kawai ya zama dole ba ne yana kuma da matukar muhimmanci a wajen samar da yara masu cikakkiyar lafiya da ilimi, hakan kuma shi ne ginshikin ci gaba da bunkasar kasar baki daya.

Haka kuma yana da muhimmanci a samar da wasu hanyoyin samun kudin shiga ga kasa, dogaro ga bangaren man fetur ba zai haifar da da mai ido ba ga Nijeriya. Dole Nijeriya ta nuna wasu hanyoyin samun kudaden shiga wanda zai samar mana da ci gaba a bangaren samar da ayyukan yi ga matasanmu da rage talauci a tsakanin al’umma.

Baya ga kokarin da ake yi a cikin gida, hadin kai da kungiyoyin kasashe waje yana da matukar muhimmanci. Dole Nijeriya ta nemi gudummawar abokan hulda na kasashen waje wajen neman yadda za a samu saukin kawo karshen rikicin da kuma yadda za a yi maganin abubuwan da rikicin ya haifar. Al’umma na da muradin ganin sun taimaka wa Nijeriya da hanyoyin magance matsalolin tare da samar da zaman lafiya don ta haka za a tabbatar da zaman kafiya a duniya baki daya.

A ra’ayinmu, wannan rahoton yana karfafa bukatar rungumar matakan kariya ne na kokarin kauce wa fadawa irin wannan rikicin a nan gaba. Samar da hanyoyin kare aukuwar rikici zai kai ga ceto rayuwar al’umma da kuma ceto tattalin arzikin kasa. Don haka bayanin cewa, an yi asarar fiye da Dala Biliyan 100 a rikincin yankin Arewa maso Gabas ya kamata ya farkar da mu, kuma hakan ya zama izna ga Nijeriya da ma Duniya baki daya a kan bukatar a rungumi hanyoyin kare aukuwar rikici ba wai sai wani abu ya faru ba a fara kame-kame.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Mun Dakile Hari A Kano Da Ka Iya Zama Mafi Muni A Tarihin Nijeriya —Irabor
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

October 17, 2025
Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya
Rahotonni

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

October 11, 2025
Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki
Rahotonni

Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki

October 11, 2025
Next Post
'Yan Bindiga

Wa Ya Yi Sulhu Da 'Yan Bindiga A Katsina?

LABARAI MASU NASABA

Likitoci

NARD Ta Yi Fatali Da Iƙirarin Gwamnatin Tarayya Na Ba Ta ₦43bn, Kuma Yajin Aiki Na Nan

November 3, 2025
Kano

Kano Ta Amince Da Naira Biliyan 8.2 Don Ayyukan ilimi, Samar Da Ruwa, Da Makamashi

November 3, 2025
Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

November 2, 2025
Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

November 2, 2025
Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

November 2, 2025
Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

November 2, 2025
Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

November 2, 2025
Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

November 2, 2025
Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

November 2, 2025
Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

November 2, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.