ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, November 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Yi Dai Mu Gani

by CMG Hausa
3 years ago

A yayin da kasar Amurka ta shirya wani babban taron tattaunawa da shugabannin Afirka a birnin Washignton D.C, sai ga shi wani sabon rahoton bincike da Gallup ya gudanar na nuna cewa, farin jinin fadar White House da majalisar dokokin kasar na ci gaba da raguwa.

Koda yake ba dukkan shugabannin nahiyar aka gayyata ba, bisa wasu dalilai da Amurkar da barwa kanta sani. Masu iya magana dai na cewa, idan ka so uwa to ka so ‘ya’yanta.

  • Kasar Sin Ta Shigar Da Kara A WTO Kan Matakin Amurka Na Hana Fitar Da Kayayyaki Zuwa Kasashen Waje

A cewar rahoton, kaso 40 cikin 100 na Amurkawa da aka tambaya ne suka nuna amincewa da kimar shugaban Amurka joe Biden, yayin da kashi 55 cikin 100 suka nuna amincewa da yadda yake tafiyar da aikinsa. Tambayar ita ce, wai me ya sa shugabannin Amurka suka gayyaci shugabannin wasu kasashen Afirka a cikin hali da kimarsu ke raguwa? Ruwa dai aka ce ba ya tsami banza.

ADVERTISEMENT

Bugu da kari, kuri’ar nuna rashin amincewa da Biden ta ci gaba da karuwa, tun watan Satumba shekarar 2021, bayan da sojojin Amurka suka janye daga Afghanistan.

A halin da ake ciki kuma yanzu, yadda Amurkawa ke nuna rashin amincewa da majalisar dokokin kasar, abin babu dadin ji ko kadan, inda kashi 73 cikin 100 na baligai Amukawa ke nuna rashin amincewa da kimar majalisar. Ko da yake tsuntsun da ya jawo ruwa…

LABARAI MASU NASABA

An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin

Tsohon Firaministan Japan Ya Soki Kalaman Takaichi Dangane Da Batun Yankin Taiwan

An wallafa sakamakon wannan binciken kuri’ar jin ra’ayin jama’a ne daga ranar 9 ga watan Nuwamba zuwa 2 ga watan Disamba, wanda Gallup ya gudanar, bayan zaben tsakiyar wa’adi na ranar 8 ga watan Nuwamban shekarar 2022.

Sanin kowa ne cewa, duk wani tallafi da Amurka za ta baiwa wata kasa, sai ya samu amincewar majalisun kasar, ga shi kuma sharhin da Gallup ya rubuta na bayyana cewa, majalisar dokokin Amurka za ta fuskanci rabuwar kawuna a cikin shekaru biyu dake tafe, bayan da ‘yan jam’iyyar Republican suka kwace ikon majalisar, yayin da ‘yan jam’iyyar Democrat ke da rinjaye a majalisar dattawa. Don haka, ta yaya Amurka za ta iya agazawa kasashen na Afirka cikin wannan hali na rudani? Koma dai mene ne, yanzu ya rage wa shugabannin Afirka da aka gayyata, su karkade kunnuwansu, don jin sabuwar tatsuniyar da za a fada musu. Dabara kuma ta rage ga mai shiga rijiya. (Ibrahim Yaya)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin

November 17, 2025
Tsohon Firaministan Japan Ya Soki Kalaman Takaichi Dangane Da Batun Yankin Taiwan
Daga Birnin Sin

Tsohon Firaministan Japan Ya Soki Kalaman Takaichi Dangane Da Batun Yankin Taiwan

November 17, 2025
Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95
Daga Birnin Sin

Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

November 16, 2025
Next Post
Qatar 2022: Rashin Nasararmu A Hannun Saudiya Ya kara Mana Kaimi – Messi

Qatar 2022: Rashin Nasararmu A Hannun Saudiya Ya kara Mana Kaimi - Messi

LABARAI MASU NASABA

Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi

Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi

November 17, 2025
An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin

An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin

November 17, 2025

MACBAN Ta Nemi Amurka Ta Cire Sunanta Daga Jerin Waɗanda Ta Ƙaƙabawa Takunkumi

November 17, 2025
Tinubu

Bai Dace Adalci Ya Zama Na Sayarwa Ba – Tinubu Ga Alƙalai 

November 17, 2025
Tsohon Firaministan Japan Ya Soki Kalaman Takaichi Dangane Da Batun Yankin Taiwan

Tsohon Firaministan Japan Ya Soki Kalaman Takaichi Dangane Da Batun Yankin Taiwan

November 17, 2025
Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

November 17, 2025
Hakimi, Osimhen Da Salah Ƴan Wasan Da Ke Takara A Ƙyautar Gwarzon Afrika

Hakimi, Osimhen Da Salah Ƴan Wasan Da Ke Takara A Ƙyautar Gwarzon Afrika

November 17, 2025
Tsohuwar Firaministan Bangaladesh Sheikha Hasina,

An Yanke Wa Tsohuwar Shugabar Bangladesh Hukuncin Kisa

November 17, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

November 17, 2025
Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka

Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka

November 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.