• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abincin Da Ya Kamata Mai Azumi Ya Ci Da Wanda Bai Kamata Ba

by Bilkisu Tijjani
1 year ago
in Girke-Girke
0
Abincin Da Ya Kamata Mai Azumi Ya Ci Da Wanda Bai Kamata Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Assalamu alaikum barkanmu da warhaka, barkanmu da sake haduwa da ku a wannan makon a cikin wata mai alfarma na Ramadan a cikin shirin namu na Girki Adon Mata.

 Watan Azumi lokaci ne da musulmi ke kaurace wa abinci tun kafin ketowar alfijir har zuwa faduwar rana. Hakan yake sa mutane jin yunwa da gishin ruwa. Masu Azumi sukan ci abinci daban-daban a lokacin sahur da na buda baki.

  • “Tutar Dimokuradiyya” Da Kasar Amurka Ta Rike Ta Lalace
  • Tsaron Iyakoki: ACG James Sunday Ya Jagoranci Taron Samar Da Dabarun Aiki A Jos

Sai dai likitoci sun bayyana nau’in abincin da ya kamata mai Azumi ya ci da wanda ya kamata ya kauracewa.

 Dakta Lawan Musa Tahir, wani likita a asibitin Nizamiye da ke Abuja, Babban Birnin Tarayyar Nijeriya, ya shaida wa BBC Hausa irin abincin da ya kamata masu Azumi su ci da kuma wadanda ba su kamata ba.

Wanne nau’in abinci ya kamata mai Azumi ya ci?

Labarai Masu Nasaba

Yadda Ake Alale

Hadin Tuwon Dawa

Masu fama da wasu cututtuka

 Masu Azumi sun kasu kashi-kashi: misali, akwai wanda da ma kafin Azumin saboda da wata larura a asibiti za a dora shi kan abincin da ya kamata ya ci ko kada ya ci.

Misali a nan shi kamar wanda yake da ciwon suga za a dora shi kan dokoki na yanayin abincin da zai ci, ko wanda yake da ciwon hanta, shi ma za a dora shi kan dokoki na abinci da zai ci, sai mai olsa shi ma akwai abubuwan da ya kamata ya ci da kuma wanda bai kamata ba.

 Haka kuma wanda yake da ‘food allergy’, wato wanda jikinsa ba ya karbar wasu nau’o’in na abinci: To, kun ga wannan tun kafin Azumi akwai dokoki na yanayin abincin da yake ci, don haka idan Azumi ya zo zai ci gaba da bin dokokin.

Mutanen da suke koshin lafiya

Sai kuma mutanen da su da ma lafiyarsu kalau, su ma ya danganta da inda suka samu kansu lokacin Azumi.

 Misali, idan mutum yana zaune a irin kasashenmu masu zafi inda mutane suke bukatar yawan shan ruwa a kai – a kai, su ma akwai yadda ya kamata su yi. Ga jerin abinci da abubuwan da suka kamata masu Azumi  su yi:

Guji cin abinci mai yaji da wanda yake da maiko sosai saboda zai kara musu kishirwa sannan akwai zafin gari. A ci abinci mai ruwa-ruwa, musamman ‘ya’yan itatuwa irin su Ayaba, Abarba, Gwanda, Kankana da makamantansu

A sha ruwan zafi kamar shayi ko koko ko kunu domin suna gyara ciki musamman bayan an dade ba a ci abinci ba. A guji cika ciki fal da abinci za ka ga wasu suna cin abinci sosai idan an sha ruwa. Hakan yana da matsala. An fi so ka ci abinci kadan sannan ka huta yadda idan an jima za ka iya sake ci.

 A guji shan taba da dangoginta saboda tana da illa. Babu laifi idan an motsa jiki lokacin Azumi amma a yi shi saisa-saisa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tsaraba Ga Amaren Bayan Sallah Da Masu Niyyar Aure

Next Post

Tarihin Masarautar Zazzau Da Sarakunanta (1)

Related

Yadda Ake Alale
Girke-Girke

Yadda Ake Alale

3 weeks ago
Hadin Tuwon Dawa
Girke-Girke

Hadin Tuwon Dawa

1 month ago
Yadda Ake Faten Acca
Girke-Girke

Yadda Ake Faten Acca

2 months ago
Danbun Shinkafa Da Nama Da Kifi
Girke-Girke

Danbun Shinkafa Da Nama Da Kifi

2 months ago
Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)
Girke-Girke

Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

2 months ago
Danbun Shinkafa Da Nama Da Kifi
Girke-Girke

Danbun Shinkafa Da Nama Da Kifi

3 months ago
Next Post
Tarihin Masarautar Zazzau Da Sarakunanta (1)

Tarihin Masarautar Zazzau Da Sarakunanta (1)

LABARAI MASU NASABA

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

September 16, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

September 16, 2025
Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

September 15, 2025
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

September 15, 2025
Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

September 15, 2025
Tinubu

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

September 15, 2025
Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

September 15, 2025
Sanata Natasha Za Ta Fuskanci Hukunci Daga Kwamitin Ɗa’a Na Majalisa

Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa

September 15, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

September 15, 2025
Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.